Da kaina na shirya zuwa, Kano don yi wa Ummata albashir, da kuma maganar bikin Maryam, Sai lokacin Allah Ya kawo nata mijin.
Ni da Hassana da Husaini na tafi, Umma kam ta ji dadin zuwana, ni kaina na ji dadin zuwan, saboda yanzu lokacin ziyarar wahala yake yi min, hidimomi sun karu, ga duk inda mutum zai je sometimes Sai da security, Amma a wannan karon daga ni sai direba mu ka taho.
Lokacin da na sanarwa da Umma albishir din da na kunso mata, ba karamin farin ciki ta yi ba, har da kuka, wai dama kullum tana. . .