Dakin Lauje ya turnike da hayaki tamkar wutar damuna.
Alhaji Aminu ya shigo gidan daidai hayakin na turiri saboda Kiran da Laujen yayi mishi. Ya zube Yana laluben laujen saboda hayakin da ya turnike dakin ba baya bukatar a sanar dashi Zubaina ce zata bayyana, Ilai kuwa sai gashi ta bayyana tana Rera kuka maimakon Dariyar da ta saba zuwa da ita "Me ya faru Kuma yau gimbiyar dodon kod'i?
Ta jima batayi magana ba kafin tace,
"Yaron wuri nane bashi da lafiya Kuma ba zai warke ba sai an Bashi tayin da baizo Duniya ba shine nake so. . .