Skip to content

San da ya sauko kasa ga mamakinsa har ta bude zata fara zuba masa, kusan suman zaune yayi bai taɓa tunanin zata sako da wuri haka ba ko ma yace gaba daya .

Zuba mata ido yayi ta gama ta bashi ta kawo ruwa ta ajiye masa sannan ta diba ita ma ta tashi zata shiga daki yace” kifin fa tace a’a kaci kawai “

Yayi murmushi ya mike ya zuba mata a gefe yace” ki zauna mana kici a nan” tace” uhumm tohm ta matsa can gefe ta fara chi ,haka har tsawan lokachi sannan suka gama ta wanke kwanikan zai fita sallar a zahar har zaija kofa tace” daman kayan miyar na ga sun lalace babu yawa masu kyau din baza su isa na dare ba ko kuma ayi shinkafa da wake?” Murmushi yayi yana jinsa a sabon ango yace “duk yadda kika ce sai ayi zan shigo da wasu in yaso kiyi abunda ya dace kawai “tace “tohm” duk maganar nan kanta a kasa take yinta ,ya fita yana tunanin me ya canzata haka .

Ita kuma dawo har ga Allah tausayinsa ne ya fara kamata duk tana jin baza ta iya zama dashi ba amma abunda tsohuwar nan take masa har ranta take jin zafi .

Bayan mintuna da fitarsa, kamar jiransa suke ya fita su Murja suka shigo gwaggo na biyo su tana cewa” kuci mata uwa dan uban ta “.

Murja ce da wasu ƴan mata uku ita ta hudu suka fara dukan Ikram ta ko ina mutane suka fara zuwa da niyyar kwatarta abun ya ci tura domin sarkin yawa yafi sarkin karfi dole wata mata tasa aka kira Haidar yana can zai tafi kamfani karbo wasu abubuwan , hankalinsa a tashe ya taftafkesu sannan ya dauketa ya fita da asibiti domin sun raunanata ta aka danyi mata treatment , daga nan baizarce ko ina ba sai gidan baba Ibrahim ya fada masa komai ransa ya baci ya tashi da kansa yaje gurin Gwaggo .

Ya same su yayi musu fada yace “Gwaggo wannan abunda saukai bai dace ba ,kuma idan har wani abun ya samu ƴarsu daure ku zasuyi kar kuga sun bashi auranta a banza idan kuka cutar da ita sai inda karfin su yakare , da haka ya kasha musu jiki domin daman shi kadai ne yake iya fada mata gaskiya komai daciinta , dan shi duniyar ba damunsa taiba indai harka wulakanci ne ko rani da san abun duniya basa sa shi aciki.

Haka ya dawo da ita duk jikinta yayi tsami ,ya dora mata ruwan zafi tai wanka ta samu ta dan sha fura da ya siyo a hanya tasha magani ta kwanta.

Haka haidar ya dinga kula da Ikram a haka har ta fara sabawa dashi domin duk wani abu baya kyashin yimata shi indai zata ji dadi musaman yana ganin a dalilinsa tasha duka .

A haka har jiki yayi sauki Alhamdulillah ta dawo normal ta dan fara aikin gida tana gyara gidan su tsab tayi musu girki.

Kamar kullum yau ma sun tashi sun gyara komai ya fita.

Tunda ya fita bai dawo ba har magrib haka ne yasa ta dora shinkafa da wake sai dai ta manta ba yaji , tana idar wa ya kwankwasa kofa ta bude nan ta ganshi da kaya niki niki da alama wani kayan abinchin ya kuma aunowa ta karbi wasu suka shige kitchen tace” sannu da zuwa” yace “yawwa nayi dare ko ? “Tace ” uhum ” yace “wani kudina na karbo shine na kuma yimana siyayyar kayan abinci saboda bana so ya yanke mana har fulawa na siyo mana” tai murmushi tace “har na dafa shinkafa da wake amma ba yaji da da inda yaji yake da an siyo kafin gobe mu daka ko?” Tana dubansa yace ” eh ba a rasa ba ga kabeji da cucumber nan sai mu hada ko na siyo mana kifi ko kwai ? mu dan dora akan shinkafar ? ” .

Tai murmushi tace ” duk abunda aka samu” yace ” to bari na bawa yaro ya siyo yajin sai nayi sallah isha zan shigo” .

Har ya juya tace” uhumm daman_daman bm bani fitila karsu dauke nepa din “yace “ba waya a hannunki? ” Tace ” eh tana gidan mu basu kawo min ba” yace “tohm ga karamar wayata sai ki dan haska kan na dawo” tace ” tohm a dawo lafiya ” .

Ya fita yana cewa “ameen” bayan fitarsa ta gyara komai taiwa kayan abinchin gurin zama ta yanka kabejin da cucumber ta zuba a mazubi mai kyau sannan ta hada lemon da ta gani ya siyo ta kai kan dinning tana jiransa, tai alwala tayi sallah.

Bayan ta idar tunani ta tafi a cikin ranta, akwai kayan da yawa datake so a kawo mata daga gidan su amma taga sunki zuwa .

Tana nan zaune har ya dawo suka zauna kan dining ya bata yaji da bakar leda da nama ta zuzzuba musu anan suka fara ci ,duk da taki sakin jikinta ya lura sai zuba yaji take da a lama tana san yaji.

Suka gama ta gyara komai dan ta tsani tara wanke,wanke ko a gida maman su ta horar da su akan hakan .

Haka suka cigaba da rayuwar su ta sauke yimasa rashin mutunchi da ta kunsa amma babu wata kyakyawar magana sai dai in yasa tayi, in ya hanata ta hanu abun ya samu da ga rashin mutumcin da gwaggonsa kullum sai tayi ta kare musu zagi tas! Ita kuma hakan yasa tausayinsa a ranta, ta rage wulakancin da tai niyyar yi, kullum ita take musu girki da yake ta horu a girki ba wanda bata iya ba har wata kiba sukayi dukkan su, saboda ba tashin hankali a tsakaninsu sai girmama juna yanzu duk ba wai kula juna suke ake hira ba.

San shima ya koma bakin aikin sa na jari bola, makaranta ce dai ya gama sai jiran sakamako .

Yau satin su biyu ciff tana zaune bayan ya fita taji wani buggun azatan ta shine tana bude taga Mamanta da sauri ta rungumeta tana murna, tare suke da kannan ta su Abba da Al’amin da kannan Mamanta suka shigo da kaya niki niki suka gaisa ta kawo musu ruwa da lemo basu jima ba suka bata duk wani kayanta da kudin sadakinta da wanda Momi ta kara mata da wanda Islamiyar su ta bata da kayan sawarta da duk wani abu da ta mallaka a gidan su wai daddyn ta ne duk yace su hado mata da wayoyinta da ya siya musu wanda abaya ya kwace ta ta yanzu ya bata akawo mata, Harda laptop din ta ita kuma kanin Momin su ne ya siya mata lokacin da daddyn su ya siyawa Najwa yaki siya mata shine shi kuma ya siya mata.

Momi ta kalleta tace” daddyn ki yace karki so ma zuwa gidan sa yanzu sai kin yi watan ni dan baya bukatar ganinki a yanzu ” Ikram ta duniyar sa kanta tana jin wani iri.

Komo tace” Ikram da kin dage da tuni yanzu kema kuna tare da Najwa gashi kin ƙi ga inda kika jefa kanki babanku nema yake ya cire sunanki a sunayan yaran sa , ki kula sosai, ni dai abunda zance miki kenan domin mahaifinki ya dau zafi sosai dake ki rke mijinki shine gatanki a yanzu dan a yanzu haka mintina shabiyar ya bamu mu koma yana jiran mu, dan haka karki sake ki wulakanta mijinki domin zai iya baki wanda ya fishi muni wallahi.

Ikram kuka take sosai suka tafi suka barta , Haudar anan yazo ya tarar da ita ya shigo alwalar azahar ya ganta tana kuka yace” me ya faru ?”tace” ba komai’ yace” kayan nan fa” tace “daga gidan mu a ka kawo kawo min ragowar kayana ne”.

Haidar yace “tohm ki dan matsar da su in na dawo sai na tayaki gyarawa” tace “tohm” .

Ya fahimci akwai damuwa akan fuskarta mai yawa amma ya zaiyi yasan bashi damar takura mata ta fada masa yace” akwai abinci ne?” tace “eh yanzu zan gama in ka fito daga masallachi sai ka karba” yace “tohm” .

Ta mike tana kokarin danne komai ta shiga Kitchen.

Haka kuwa akayi bayan ya idar ya shigo karba ya tarar bata karasa ba ,sai yace” bari na dan tayaki” tace ” toh tana murmushi ” .

Suka fara aikin tare suna hira jefi-jefi sun fara sun kusa kammalawa ma sai ga gwaggo ta shigo.

Ikram tana fitowa daga kitchen shima yana biye da ita ta karaso kusa dasu ta bude baki tana tafa hannu tace” lallai Aliyu wato tare kuke yin girkin halin ubanka dai duk ka dauke shi kaima bawan mace zaka zama Ali?”.

Nan fa ta inda ta shi bata nan take fita ba , su dai suka tsaya suna kallonta dan ko Ikram inda sabo ta saba da masifar matar dan kwanaki taje gaisheta kusan dukanta tayi tace batasan gaisuwar

Bayan ta gama masifar ta lalle shi tace “kudin mota zaka ban zanje unguwa kuma 1000 zaka ban wallahi zuwa da dawo wa” baice komai ba ya curo 1000 ya bata yayi gaba .

Ta kalli Ikram tace “ke kuma jinin mayu ƴar sadaka ki kiyayeni dan ni nafi karfin matsiyacin mijinki wallahi, kuma daga yau duk abunda kuka dafa kikai min ko kuma zan dinga turo yaro yana dauka”. Ita dai Ikram bata ce mata komai ba , ta shige dakin su , nan ma zagi ta afkamata sannam ta wuce ta banko musu kofa.

Abinchin da ta zuba masa a cooler ya dauka yace “sai na dawo ” tace “dan Allah karka kace sai gab da magriba zaka sake shigowa ” murmushi yayi ko bakomai itama fara damuwa da shi yace” tohm “.

Rayuwar su ta zama abun burgewa idan bakasan yadda suke zaune a badini ba ,dan sai ka zata auran so da kauna ne ,dan zagewa yake ya tayata aiki duk da ba wata hira suke ba .

Gwaggo kuwa kullum za a kaimata abiuncin kullum kuma sai ta kushe shi, kuma a haka duk yaran ta sunsa matansu -su dinga kawo mata abincin , wani zubin har yawa yake amma duk randa Ikram bata gama da wuri ba, ta da kwanciyar hankali domin sai tazo ta karewa iyayyansu tas.

Yau ta gama wanke wanke da shara ta gama suna zaune tasa kaya tana so tace masa wanki ko zai bawa wani yayi domin kayan sunyi datti bataso tayi da kanta , amma taji yana complain bashi da kudi a kwanakin nan da yana waya .

Ta zauna ta zuba wa kayan masu datti ido da tuni ta kaiwa idi mai wanki ko ta jefa su chikin injin wanki , nan da nan idon ta ya kawo ruwa .

Kiran ta yake yaji tayi shiru ya karaso ciki ya ganta ta zubawa kaya ido yace” wanki ne haka suka taru ?” tace “eh” yace “yau daman bazan fita da wuri ba ,bari na dibo ruwa ayi wanki nima nawa ya dan taru “.

Ya fita ta bishi da kallo nufinsa ita zatayi ko shi zaiyi mata ? Ta dai zubawa sarautar Allah ido.

Shigowa yayi yace” bari na samo mai ruwan dadi” tace “tohm” ya fita ya samo yace “ta fito da wankin” ta fito dashi ya zauna tana kallonsa tace” kai zakayi?” Yace “kayan da basu kai kala goma ba ko takwas kike mamaki bari kiga kafin ki rufe ido ki bude na gama” dariya ce ta kufce mata wanda hakan ya dauki hankalin sa ya shagala yana kalonta tace “me zan tayaka to?” Yace “uhum ki zauna ki ta kalona kawai” tace “ai bazan iya ba” nan ta fara ta yashi dauraya in ta kasa matsewa ya karba yayi sunayi suna dan hira ,suka gama yace ” dauko daddumar nan ma a wanke ta” tace” kai wai baka gaji ba?” Yace” Ai naga tayi datti munayinta sai mu tashi ” tace “tohm” .

Wannan karo tare suka wanke daddumar suna cikin matsewa yace ta rike gefe ya matse sai ga gwaggo ta shigo .

Aikuwa ta rike baki tace” tab!! Abun naka hauka ne Ali wato kai kafi ubanka ma wanki kake mata , banzan munafiki in nace kaimin wanki sai kace kaza da kaza ko kayi kana kunkuni amma nan kazo karamar yarinya waca ka kusa ninka shekarunta kana mata wanki ” ta jiyo kan Ikram tace” ke kuma munafuka ni nasan ba banza ubanki ya bada sadakar ki ba daga gani ke mayyace wato zaki makalewa jikana toh wallahi in ma wani abun kikeso bazaki samu ba lokaci nake jira na daura auransa da murja jininsa nai masa auran gata ba irin wulakantacan auranki ba dan haka ki sakar masa kurwa ya wala” . Ta dawo fuskar ta kan Haidar tace” kai kuma abunda ya shigo dani shine naji balarabe yace kaje masa da maganar sauran gadonka wai zaka ja jari koh?’toh na cinye domdomin ko yana nan bai isa ya kwata ba bale kai ,ka godewa Allah da ka tsira da wannan gidan ma, banza wawa dan wawiya ance maka gadon na ka ne kai kadai ,zaka kawo mana zancan banza toh baza a bayar ba ,lokachin da ubanka ya samu kudin da taimakon su wa ya samu, munafiki shiyasa na nace kar uwarka ta dauke ka da ban san kalar munafurcin da zakai ba, yanzu ma gashi ka kware tunda ka tsotso a wajan uwa”.

Ta juya ta fita, Ikram tsorata tayi ganin yadda jikin sa yake rawa ga idonsa yayi mugun ja tace dan Allah kayi hakuri tuni kuka ya kufce mata ta dawo kusa dashi ta dafa shi ,shima bashi da zabin da wuce kukan dan haka a hankali idan sa ya dinga zubar da hawaye da kyar ta dinga bashi hakuri ya mike baice komai ba ya shiga daki ya kwanta ta karasa shanyar daddumar ta gyara tsakar gidan ta dora musu girkin rana domin rana ta farayi haka ta gama girkin sukuku dan yau ko sallah azahar gida yayi kuma yaki magana sai dai taga idan sa na zubar da hawaye.

Wasa wasa haidar gaba daya ya daina walwala a gidan in ta kawo masa abinci godiya kawai yake mata gaba daya ya canza kusan kwana uku, abun yana damunta sosai ta saba da yadda yake mata ya saki jikinsa da ita yayi mata dariya duk damuwar da take ciki dalilinsa damuwarta ta fara raguwa amma shi gashi yana cikin damuwa ta ma rasa yadda zata shawo kansa fita ma in ya fita baya dadewa sai ya dawo gida ya kwanta,hankalinta duk ya tashi.

Yau tana zaune akayi sallama haidar yana nan kafin tayi magana ya fito yace” waye ?”sai akace” kaya aka kawo ma” yace ” tohm” ya fita.

Bai dade ba ya dawo can yamma ya kara fita ya dawo sai ga shi an kara buga musu kofa , tayi tuna nin almajirin da ya aika siyo pure water ne sai ta bude sai taga wani yaro wai haidar yazo tace inji wa? Yace ” ‘yan sanda ne a mota sukazo” gabanta ne ya yanke ya fadi tace” mai zai musu?” Kafin yaran ya sake magana suna daga murya da cewa” zamu shigo idan bazaka fito ba malam”. , Innalillahi wa’innailaihi raji,un ta ambata tace “kace yana zuwa” .

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.