Skip to content
Part 13 of 22 in the Series Jahilci Ko Al'ada by Harira Salihu Isah

“Allah shi ne kuma nima naji mamaki na tambaye sa Ammi fa sai yace bari ya dawo daga masallaci zai yi latti”.

“To Allah dawo da shi lafiya dan na mastu na kalli Ammi”.

“Amma fa inaga shi kaɗai yazo dan yace mun mu shirya kamun ya dawo wataqilan zai kai mu wajan Ammin ne”.

Yana ficewa a gidan ya ɗauki motan sa qirar Toyota mai tinted glasses ya mata key sai babban masallacin juma’a na qofan Sarkin Gombe.

Yana zuwa Allah ya taimake shi ba’a fara salla ba nan ya samu ya lallaɓa har wajan liman da ya idar da khuɗuba suka gaisa cikin mutuntawa ya faɗa masa buqatan sa, nan limamin yace masa mahaifin sa ya jima da masa magana kuma suna kan addu’a, godiya yawa limamin sannan ya bada kuɗi a sayi abun sadaka 2million ya basa check dan dama tun a gida ya rubuta check ɗin.

Suna gama magana da liman ya koma wajan zaman sa ya zauna jiran a tada Salla yana danna counter (carbin qirge) zuciyansa cike da tunanin dama Abiy ya damu da ɓatan Ammi ne da har ya bada ayi addu’a? Inda gefe ɗaya kuma yaje cike da taqaicin zuwan su sweetie Nigeria.

Ajiyan zuciya ya sauqe jin ana qiran sallah sai ya miqe shima ana idar da Qiran kamun a tada iqama ya jero addu’oeen sa ya shafa aka tada sallah.

*****

Manzon Allah SAW yace “ku kasance masu miqa addu’oeen ku ga mahaliccin ku Allah maɗaukakin Sarki a ko wanni lokaci sannan mafi soyuwar lokaci ita ce yayin da liman yake tada iqama na sallahn asuba da kuma ranar juma’a domin kuwa a ranar juma’a akwai wani lokaci wanda ke ɗauke da sa’a wanda duk wanda Allah ya nufa yayi addu’ansa a wannan lokacin ta sa’ar to ba hijabi tsakanin karɓuwan addu’an sa ga Allah”.

To sai malamai ke cewa wanne lokaci ne wanda Annabi stira da amincin Allah su tabbata a garesa ya ambata? Wasu daga cikin malamai ke cewa sa’ar na nan lokacin sallar asuba ta ranan juma’a, wasu kuma suce tana nan a lokacin da liman ke qiran sallah kamun kuɗuban farko wasu kuma suce kuɗuba na biyu wasu kuma suce yayin ta da iqaman sallahn juma’a.

Mu qwata wunin juma’ar mu da zikiri da ambaton Allah da kuma yawaita salati ga shugaban Annabawan Allah Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam ♥️

WALLAHU A’ALAM.

*****

Suna idar da Sallah, aka ɗaura aurarraki aka yi addu’a sannan liman ya roqi jama’a da a taya su da addu’a akan ɓatan wata baiwar Allah, nan aka kuma addu’a aka shafa.

Yana fitowa yayi ta aikin raba sadaka, dama halinsa ne kyauta duk ranan juma’a kuma yana sadakan kuɗi wani bin har da abun ci.

Yayi wa masu Dabino da Alewa juye kowa ya raba sadaka sannan ya shiga motan sa ya ja ya nufi anguwansu GRA.

Mama mai aiki tana fitowa kitchen tayi mummunan gani, dan a wajan ta wannan mummunan gani ne dan tulin jarabar da yau zata kwasa akan wannan aika-aikan, kulan ferfesun Abiy a yashe a qasa.

Cikin hanzari take qoqarin tattare wa kamun aunty amarya ta fito ta gani ta fara mata tijara, amma sai aka yi rashin sa’a tana cikin share wajan Aunty Amarya ta fito.

Kallon mama mai aiki tayi sama da qasa tace “me wannan ya zube?

Cikin in e na tace “ha…ha… Hajiya ayi haquri nima wa…wall….wallahi bansan da.. da wannan aiki ba sai yanzu na gani”.

Malalacin kallo ta wasta mata sama da qasa dan ko ba’a faɗa ba tasan ferfesun Abiy aka zubar kuma daga maganan mama mai aiki ta gane Munawwara ce ta zubar, dan haka rai a ɓace tana huci ta nufi sashin Ammi.

Ba sallama ta tura qofa ta shiga tana haqi tana huci kaman za taci babu, tana qwala wa sweerie qira “Keeeee! Keeeee! Munawwara”.

DMD da ya iso gidan ya buɗe qofan palourn kenan ya shigo sai yaga bayanta ta shige sashin Ammin sa kuma ta banko qofa, rai a ɓace ya buɗe qofan sashin ya shiga amma sai ya tsaya a bakin qofa yana qare mata kallo jin irin qiran da take wa sweerie kaman ita ta raɗa mata sunan, tsayawa yayi ganin iya gudun ruwanta.

Bata san da shigowan sa palourn ba ta ci-gaba da cewa “Munawwara! Munawwara! Keee Munawwara ba ke nake qira ba?

Cikin sauri Munawwara ta fito a ɗakin, sanye take cikin dogon riga wanda bai kama jikinta sosai ba bai kuma mata ruwa sosai ba, idanuwan ta akan Darling dake staye bakin qofa suka sauqa amma sai ya mata alama da kar ta nuna ta gansa.

Cikin qufula Aunty Amarya tace “ke dan uwarki ba ke nake qira ba kika yi banza da ni? Ina wasa da ke ne zaki zubar da abincin miji na dan nace kije ki taya ta girki wato gaki fistararriya ko? Tunda ba Uwarki ce ta sanya ki ba dole kimun ta’adi tunda buri kuke ubanku ya sake ni ya zauna da uwarku kawai kuna taya ta kishi ko?

“Kiyi haquri Aunty ba da sanina bane ya faɗi a hannuna kiyi haquri” Munawwara ta faɗa idanuwanta cike da ƙwalla sakamakon masifan Aunty Amarya, dan su basu saba da masifa ba balle stawa, Ammi bata musu Abiy ma haka Darling ma haka.

Tsabar masifa Aunty Amarya har qanqance ido take kaman zata rufe sweerie da duka, cewa tayi “Har zaki ce bada saninki ba dan uwarki” ɗaga hannu tayi zata sharara mata mari amma kamun hannunta ya kai ga sauqa sai taji an riqe hannunta an buge gefe, cikin taqaici ta juyo za tayi ashar amma ganin waye ne sai ta haɗiye zagin tace “kai har ka isa ka hanani hukunta yarinya tamun laifi ina matar ubanka ni sa’arka ce da zaka riqe hannuna?

Kallon sama da qasa ya mata ya watsar da kashin ta kamun ya juya ga sweerie yace cikin Indianci “dama bance ku shirya bane ko reni ne? Wuce ki qira sweedy ku fito yanzun nan” ya faɗa yana zama a kan ɗaya daga lumstuma-lunstuman kujerun palourn Ammi.

Cikin taqaicin rashin ida nufinta ta juyo ta kalle sa tace “ina maka magana ka maida ni mahaukaciya amma ai kasan nima uwarka ce b….” Wani kallon da ya mata ne ya sanya ta haɗiye maganan dake bakin ta tana ja baya dan ta storita ganin yanda lokaci guda ya sanja fiska da irin kallon da yake mata.

Yatsa ya nuna mata kaman wanda bakinsa ke ciwo yace “watch ur tongue” iya abinda ya faɗa kenan ya fidda wayansa yana lastawa.

Cikin stiron masifa da ke cinta da ayyana irin abinda zata faɗa wa Abiy ta fice a sashin fuuuuu ta banko qofa.

Guntun tsaki yaja “mstwwww! Idiot human being bansan shima me ya gani a wajan ya burge sa ya auro ta ba” ya faɗa yana taɓe baki.

Sweerie da sweedy suka fito yace musu “ina key ɗin Ammi?

Sweedy ne ta miqa masa ya karɓa ya sasu gaba suka fice yaja sashin ya rufe ya jefa key ɗin a aljihun sa suka fice a gidan.

Suna fitowa a palourn a compound na gidan suka ci karo da Abiy da sweetie sun dawo hannunta da ledodi alaman siyayya ya mata.

Sweetie da gudu tayi wajan Darling ta rungume sa tana cewa “Darling ina ka baro Ammi” kallon ta yayi kawai ya kau da kai ya juya dan zuwa yanzu ya fahimci me Abiy ya faɗa musu ba sai ya tambaya ba.

Abiy ganin ko kallon sa be yi ba sai ya kai kallonsa kan su sweedy yace “Munawwara where are you going?

” Darling ne yace mu shirya ya kaimu mu gaishe da mummy” qarya ta sharara masa dan ita ma bata san ina zasu ba kawai ta faɗawa Abiy hakan ne.

“To ku dawo lafiya ku gaida mummynku” Abiy ya faɗa yana shigewa cikin gida.

Dukansu ɗuruwa suka yi seat na baya, har ya sawa mota key sai ya fasa tayarwa da Indianci yace “waye drivern ku?

Ba shiri sweetie da ke gwalalo ido ta fito dan tasan ko yaushe ita ce da zaman gaba, yanzun ma dan taga ransa a ɓace shiyasa ta storita ta shige baya.

Qwafa yayi yaja motan suka fice a gidan sai Tunfure.

A bakin gate yayi parking dan sharp-sharp yake so su gama su fito, cikin gidan suka shiga suka tarar mummy na saving Daddy da abinci.

Da gudu sweetie tayi wajan Daddy ta rungumesa, yana murmushi yace “manyan mata yaushe a gari?

Sweetie na dariya na farincikin ganin Daddyn ta washe baki tace “Daddy yau da sassafe”.

Mummy na murmushi ta rungume su sweedy tana tambayansu wa ya kawo su?

Sweedy tace “Habibty Abiy ne ya kawo mu”

“Masha Allah Abiy ya kyauta sannunku da hanya”

Daddy sai biyewa sweetie yake, ta ɗau cokalinta suna cin abincin da aka saka masa tare.

Sweedy ma mummy ta saka mata ita kuwa sweerie tace ta qoshi dan ta gama cika cikinta a kitchen da ta taya Mama mai aiki girki.

DMD ma yace ya qoshi, sanin hali ya fi sanin kama dan haka mummy bata masta masa ba mutumin da kaman bai da halittan ƴaƴan hanji a cikin staɓar rashin son cin abinci kuma Allah ya taimake sa ulcer bata kama sa ba.

Sanda suka gama cin abincin suka ɗan huta dan sunyi awa a gidan kamun ya duba lokaci ganin yamma na yi ya dube su yace “maza ku tashi mu tafi”.

Daddy ne ya kalle sa yace “har za ku koma gida son? Ni na ɗauka kwana za suyi kuma ai ko ba kwana ba ka barsu sai zuwa dare ko?

Kaman baison yin magana yace “Daddy ba gidan Abiy za mu tafi ba kar dare ta mana a hanya”.

“To ina zaka kaisu son? Cewar mummy da idanuwanta ke kansa.

“Habibty Ashaka zan kai su kuma a yau nake so na dawo”.

“Ashaka dai son? Shi Mustaphan ne yace ka kai su ko kuma me daga zuwan yara basu huta ba ka sanya su a hanya”.

“Daddy gidan Abiy ne sai a hankali kasan abinda ya ajiye a gidan”.

Mummy tace “duk da haka dai son bai kamata ba shi mahaifinku ne kuma gidansa naku ne ba matar da zata sanya hijabi tsakaninku da abinda yake mallakin ku, ka dinga haƙuri don dama mu mata sai a hankali”.

Shiru yayi bai ce komai ba sai Daddy yace “shikkenan son na fahimce ka ku dawo lafiya amma ka kasance mai haquri da kuma biyayya ga iyaye kai ne babba abinda kayi shi suma qannenka za su gani su bi”.

Sallama suka wa su Daddy ya sa qannensa a gaba suka fice, suna shiga motan yaja da mugun gudu dan so yake ya kaisu ya dawo da wuri ɗaga waya yayi ya qira layin Jay.

Jay na ficewa a gidan Hajja ya ciro waya yayi dialing layin abokinsa da yayi saving da “Farooq” qiran na bugu ɗaya aka ɗauka.

“Hello freind yau kayi mafarki nane?

Jay dariya yayi jin abinda abokin nasa ya faɗa sai yace “kaman kuwa ka sani, yanzu dai kana ina?

“Ina gida”

“So na shigo Ashaka ne mun kwatancen inda kake nazo dan nasan gida na bajoga”

“Okay ba kasan best way international school na nan cikin Ashaka ba?

“Yeah! Na sani”

“Okay in ka shigo makarantar ka qira ni”

Jay yace “okay freind” sannan ya kashe wayan ya juya kan motan sa yayi hanyan makarantan su Afrah.

Yana isa yayi dialing layin abokinsa ya faɗa masa ya iso ya kashe wayan, yana tsaye ba jinawa sai gashi ya iso yana murmushi ya miqa masa hannu suka tafa yace “freind ashe ka shigo Ashaka shiyasa ka qira ni, amma wa ya gaya maka ina Ashaka”

“Munyi magana da Waleed ne yake faɗamun kazo service Ashaka to banma san a nan makarantan kake ba ai da na baka aikin yi domin anan Auta ke karatu kuma bata ji”

Quarter’s suka qarisa, Farooq ya buɗe qofan ɗakin sa, room and palour ne sai kitchen, ko ina a share fes-fes gwanin sha’awa, suka qarisa shiga yana cewa “dama anan Auta take karatu kenan? Amma wani class take?

Jay taɓe baki yayi yace “kaman dai a Jss 1 take ne ko SS 1 tsakanin biyun dai”

“Ai kuwa in SS 1 take to a ajina take dan yanzu presently ni ne form-mastern su, amma me sunan ta?

Hararansa Jay yayi yace “za kace baka san sunan Hajja Afrah take da shi ba ko kuwa sunan Daddy ne baka sani ba?

Farooq na dariya yace “sorry freind na tuna FATIMA NURA right? Amma ba mai sunan sai dai wata me suna FATIMA NURA MUHAMMAD”.

“Dan renin hankali ita ce to tunda baka san tana aiki da sunan Alhaji ba”.

“Ai kuwa sai yanzu ma ta faɗo mun kasan ba cika kallon students nake ba yanzu ɗalibai renine da su in ka sake kaɗan su renaka wasu suce suna sonka wasu kuma su maka sharri a wajan qawayensu akan kace kana sonsu alhali ba haka bane”.

Murmushi Jay yayi yace “kai dai faɗa gaskiya kasan dai na sani wannan AL’ADA ce ta malamai soyayya da ɗalibansu to kai faɗamun akwai wacce ta maka a students naka?

Farooq hararan Jay yayi yace “taɓɓ JAHILCI KO AL’ADAH? Kana Malami kayi soyayya da ɗalibar ka ba dai AL’ADA ba sai dai ko JAHILCI dan reni ne zalla gwanda ma in ɗalibai suka gama ka bi yarinya har gida in ta maka, thought akwai wacce suke zama da ita Afrah a class ina tunanin qawarta ce yarinyar nistuwan ta da hazaqanta na burge ni amma ba ina nufin wani abu ba dan duk ajin qwailaye ne irin nata ma yayi muni don ko Afrah ta fita cika ido”.

Dariya Jay ya saka har da kama ciki yace “kaji ɗan iskan malami ba, wai qwailaye wato ido kake sawa ɗaliban ka?

Hararansa Farooq yayi yace “in nasa musu ido in kalli me? Ko ita ma wannan yarinyar ba wai sonta nake ba dan karkaji nayi magananta, ni ba ruwa na da soyayya da ɗaliba dan malamai masu irin haka ke ɓata ma saura suna, kaga malami yana bin ɗalibansa ba kunya balle storon Allah wani ma har yaje ya ɗirkawa yarinyar mutane ciki sannan a haka ya qira kansa a malami wanda aka bawa amanan ɗalibai, ai Allah shirya mana al’umma kawai amma wannan halin malaman namu da wasu ke masa kallon AL’ADA tamu ta malamai to bai haɗu ba dan bakomai ciki face cikakken JAHILCI, kuma abun haushin sai kaga sun manta da suma iyaye ne su dinga bin yaran wasu wanda suma in akawa nasu ba zasu ji daɗi ba, sai dare kaga malamai suna shigowa ɗaukan yaran hostel kaman wani College ko University dan tsabar lalacewan zamanin mu ta yau, to Allah kyauta ya shirya mu amma ni Umaru ba ruwana da harka da ɗalibai dan bana qaunar reni ma”.

Jay cike da shaqiyanci ya ce “to in ba sonta kake ba me kake? Kaga in ta maka kawai faɗamun muje har gidan su in yaso sai ka rene ta kar ka damu da rashin girman ta, kawai ta girma a hannunka in kana zuba mata takin asali (sperm) tun yaushe zata girma kaman kazar gona, kai soyayyan aure zaka mata ba na lalacewa ba dan haka kai daban sauran malamai daban, Allah shirya mu duka”.

“Kai dai ɗan iska ne Jay Allah kawo maka sauqi dan fa baka ga yarinyar ba ta haɗu kam amma ba komai a wajan ni kuma tsakani da Allah yacce na balaga na balagen nan ai duk wacce na samu kasan ba aikin wasa zan mata ba balle akai ga maganan reno, sai dai ko in kai zaka iya haqura kayi renon tunda ɗalibata ce sai ka fara kamun qafa”.

Jay ya buɗe baki zai yi magana sai qiran da ya shigo wayansa ya kaste sa, ganin mai qiransa DMD sai ya ɗauka ya kara a kunne yana cewa “hello dude an tashi baccin ne?

Guntun tsaki DMD yaja yana driving, a taqaice yace “kana can har yanzu?

“Eh inanan amma bana gidan Hajja naje wajan freind”.

Da yake DMD yasan wanda Jay ke qira freind sai ya kaste qiran ba tare da yace komai ba ya ci-gaba da driving da gudu, ba jimawa suka isa.

Gidan ba za’a ce masa babba har can ba amma duba da ba’a cikin gari yake ba to zai iya amsa sunan babba kuma stararre wanda a kaf anguwan babu irin sa.

Bai ko shiga gidan ba ya tsaya a bakin gate ya juyo ya kallesu yace “ku sauqa ku shiga kuma kar naji kar na gani fatan kuna ji na?

Duk amsa masa suka yi sannan suka sauqa, sanda yaga shigansu kamun nan yaja motan sa yayi gaba.

Layin Jay ya qira ya masa kwatancen inda suke, yana shiga makarantar ya tarar da su suna jiransa, dan sanin halin DMD basu bari ya iso ya qirasu ba suka fito jiransa.

DMD kallon Farooq yayi yace “yanzu kai a nan kake rayuwa? Service ɗin nan dole ne?

“DMD ba zaka gane bane”.

Taɓe baki yayi ya shige cikin ɗakin ya ɗauro alwala ya dawo palourn ya same su suna hira sai ya shumfiɗa darduma ya ta da sallah.

Yana idarwa ya kallesu kaman wanda aka sa dole ko aka shaqe yace “kunyi sallan ne ko kun tsaya hiran mata?

Jay hararansa yayi cikin wasa yace “ba zancen mata ba cin mata muke ɗan renin hankali mutum sai kace mata-maza nikam anya dude lafiyan ka? Anyama kana jin feelings?

Ko kallo Jay bai ishe sa ba balle ya tanka ya juya yaci gaba da qirga countern sa.

Farooq dariya yayi har da kama ciki ya ce “kai fa Jay shahararren ɗan iska ne baka da magana sai na mata ai kam matarka ta shiga uku, yanzu angaya maka su mata-mazan basa jin feelings ne? Suma feelings gare su mai qarfi ma dan kaji kuma DMD irin su da kake ga suke shirun nan kaman abun bai damesu ba to sune oganni in suka kama mace sai sun sumar irinka kuma kuna good 5mints kun gama”.

Wani kallon banza kallon bakasan me kake faɗa ba Jay yayi wa Farooq ya ce “amma tabbas in nace baka ci tuwo akaina ba to nayi qarya dan tsaban renin hankali ka dubeni jibgege da ni kana qiran 5mints ai wallahi yanda nake ji na ɗin nan in mace ta shiga hannuna sai an ɗinka ta, muga wannan kala muga wannan duk muyi ittaqillah mu haƙora ai in muka samu namu ta sunna da lada to sai mun qarar da arna dan kisa, kai dai kawai ayi shiru, ɗazu Afrah ke ban labarin wata qawarta inaga ma ita kake nufi Afrah yarinyar nan dan staɓar tana ji ta fara girma har da cemun wai na auri qawarta tana da hankali amma kuma na kawo kunne ta faɗamun wata magana, duk ɗauka na wata serious magana ta arziƙi za ta faɗa mun ashe yarinyar nan cewa za tayi qawar tata bata da ko nono, to sai ka tuno mun da Afrah nima kaman DMD nake da ra’ayi sai qosashshiyar mace kuma nunanniya wacce tasan ta amsa suna budurwa dan yarinya ba za ta ɗauki buqatar Jay ba”.

“Hhhhh! Jay Allah kawo maka sauqi” faɗin Farooq yana miqewa.

DMD kallon Jay yayi ya aika masa da harara dan maganganun nasu sosai ya cika sa fam da haushi amma rashin son hayaniya yasa bai yi magana ba.

<< Jahilci Ko Al’ada 12Jahilci Ko Al’ada 14 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×