Skip to content
Part 16 of 24 in the Series Jahilci Ko Al'ada by Harira Salihu Isah

Jay ne ya shigo ɗakin ya nufi inda yake kwance yana qiran sunan sa “Dude! Dude! Dude…”

Kasancewan bashi da nauyin bacci tun shigowan Jay qaran qofan ya tayar da shi, idanuwan sa a kulle yace “Jay meyasa ka cika rashin ji ne? Ka qira mutum sau ɗaya bai yi ba sai ka qarar min da suna” yana gama faɗa ya miqe ya zauna yana laluɓo wayansa.

Jay taɓe baki yayi yace “daɗin abun ba sunanka na qira ba, koma dai mene tashi mu tafi gida”.

DMD bai ce komai ba ya miqe ya shiga toilet ɗin dake ɗakin, can ya fito yana gyara hannun rigansa da ya nannaɗe.

Bai ko kalli Jay ba ya shumfiɗa darduma ya tada Salla, sai da ya idar ya naɗe darduman sannan ya kalli Jay yace “let’s go” yana gama magana ya fice a ɗakin.

Jay miqewa yayi ya bi bayansa bayan ya kulle qofan office nasa.

Kowannen su motansa ya shiga suka yi gidan Daddy.

Ɗaya na bin ɗaya haka duka taho har suka iso gida gate man ya buɗe musu gate suka shigo kowa yayi parking suka nufi cikin palourn da sallama.

Mummy da ke zaune tana waya wanda daga ji kasan akan business nata ne, tana gama magana ta kaste tana amsa sallaman yaran nata fiskanta ɗauke da murmushi “wa’alaikumussalam sannunku da dawowa mazajen Hajja”.

Jay ne ya fara magana “habibty gaskiya nidai ba zan iya da fitinan stohuwar nan ba, nabar wa dude kyauta”.

DMD hararan sa yayi sannan ya buɗe baki kaman baison magana yace “Habibty yunwa” da Indianci yayi maganan.

Mummy na murmushi tace “yanzu son ai ko sayar da ni kayi niyan yi sai dai ka saida ni har ka amshi ƴan canjinka, dan ban fahimci ko kalma ɗaya a maganan ka ba, wannan yaren sai ku ai tunda Amminku taqi koyamin”.

DMD murmushi yayi jin abinda mummy tace, sai ya tuno rigimansu da Ammi watarana akan indiancin

** Ammi ce tayi magana cikin harshen Indianci “habibty wai Hajja na magana mune muka hana yaranmu yin aure sun girma suna gaban mu”.

Mummy idanu ta zubawa Ammi kawai bata ce komai ba.

Ammi ta kuma magana cikin harshen turanci “wai baki ji me nace ba habibty?

Sai sannan mummy tayi magana da turancin itama “ta ina zanji abinda kika ce Ammin su, bayan kinqi koyamun kuma dai so kike muyi gulmanmu amma kinqi koyamun yaren da za muyi gulman gashi ke kuma bakya jin yaren mu duka”.

Ammi murmushin ta mai stada tayi tace “karki damu yaronki zai koya miki tunda shi yana jin yaren ku yana jin Indiancin” cewar Ammi da turanci.

Muryan mummy ne ya kaste masa tunani “Son me kake tunani tun ɗaxu ina magana shiru? Mummy ta faɗa tana kallon DMD da ya faɗa duniyar tunanin mahaifiyar sa.

Lumshe ido yayi ya buɗe su a hankali yace “ba komai habibty”.

Mummy ba dan ta yarda ba tace “shikkenan, kai kuma jabeer maza-maza kaje ka ɗauko min yarinya tunda gobe Wednesday hutun ya qare akwai school”.

Jay langwaɓe kai yayi kaman mace yace “Habibty zan ɗauko ta dole na, amma nima ki dinga cemun yaronki, kowa daga son sai daughter sai yarinya na, nine kawai ake qira da sunana jabeer”.

Hararan sa mummy tayi ta wuce dinning tana faɗin “son zo kaci abinci shi kuma in ya gama kishi da yaran nawa sai yazo ya ci shima”.

DMD kallon sa yayi tare da yin murmushin gefen leɓe “ka daina kishi da mu”.

Jay taɓe baki yayi yace “ayi kishi da kai akan me? Ni wuce muje muci abinci”.

“Kaci abinci a ina bayan baka yi sallah ba”.

Jay hararansa yayi yace “in kai ke amsan sallahn in tawa tazo ka dawomun da ita, kana sharar baccinka nayi sallah kace banyi ba”.

Dukansu miqewa suka yi suka nufi dinning ɗin, mummy tayi saving nasu duk suka yi shiru suna cin abinci.

Bayan sun kammala suka miqe suka haura sama kowa yayi ɗakinsa dan ya wasta ruwa.

DMD yana shiga ɗakin sa ya cire kayan jikinsa sannan ya ɗaura towel ya shige toilet, can ba jimawa ya fito ɗaure da towel ɗin a qugunsa daga leman ruwan dake jikin sa kasan wanka yayi.

DMD namiji ne iya namiji wanda kana ganinsa kaga ingarman namiji domin ya tara duk wani abu da mace ke buqata a wajan mijin aure, Allah ya hore masa kyau ga kuɗi sannan mutum ne mara hayaniya, yana da tsayi amma ba stayi mai muni ba sannan yana da jiki wanda tsayin sa ya ɓoye jikin sai komai ya tafi dai-dai, qirjinsa mai cike da haiba a cike yake da kwantattun gashi wanda kai kace gashin kan jariri ne ba kaman na wasu mazan kaman quda-quda ba, yana da haske sannan yana da yalwan gashin kai da na gemu waɗanda suka sha gyara, gashin kansa kuwa kai kace mace ce, yana da hanci mai stayi dai-dai da kuma bakin sa wanda bai da girma sosai mai tafiya da yanayin sa na rashin son yawan magana, DMD kyakkyawa ne ajin qarshe kana ganinsa kaga wanda ya haɗa jini da larabawa ko kuma indiyawa.

Ba tare da ya staya shafa mai ko kuma sanya kaya ba ya nufi kan gadon da towel dake qugunsa, kishingiɗa yayi kansa akan fillow dake jingine da kan gado, ya sanya hannayen sa duka biyu ya tallafo ƙeyarsa yana tunanin rayuwan da suke ciki da kuma qaddaran da ya sauqa kan mahaifiyar su.

Lumshe idanuwan sa da suka koma jajaye yayi a hankali ya furta “Ammi nayi kewanki sosai, ki dawo gare mu Ammi mu koma Canada muyi rayuwanmu kaman baya hankali kwance, I soo much miss you Ammi”. 

*****

Waiwaye Adon Tafiya!

Cikakken Tarihin DMD!

Asalin labarin… 

Alhaji Muhammad Nura mai fata shine asalin sunan kakan su DMD, haifaffen garin Maiduguri ne a local government na Wuba anguwan Askira, Alhaji Muhammadu ya kasance yaro ɗaya tal da Allah ya bawa iyayen sa Malam Nura mai fata da kuma mahaifiyar sa Zainabu wacce ake qira da Yah-gana, ya taso cikin soyayya da qaunan iyaye wanda suka kasance daga cikin yaren bare-bari waɗanda aka fi sani da Kanuri.

Iyayen Alhaji Muhammadu auren dangi suka yi wanda hakan yake AL’ADAH a gare su, mutum ba zai yi aure ba sai ƴar dangin su kuma ta kasance Kanuriya gaba da baya haka ma mace sai mijin ya kasance Kanuri, Alhaji muhammadu tun da ya mallaki hankalin kansa ya nuna yana son wata yarinya a wani yanki Magumeri itama Kanuriya ce amma ba a familyn su take ba, iyayensa sun yarje masa neman ta amma da suka je wajan kakannin sa sai suka nuna basu amince ba an masa mata kuma ƴar gidan yayan maman sa. kasancewan sa yaro mai biyayya da jin magana ba musu ya amince kuma ya rabu da wacce yake so inda ba jimawa aka masa aure da FATIMA da ta kasance yarinyar kawun sa.

Bayan auren su bai wuce da shekara guda ba mahaifin sa da mahaifiyar sa suka yi hastari inda ko shurawa basu yi ba suka ce ga garinku nan (Allah musu rahama).

Kakan sa ya nemi da ya koma cikin Maiduguri ya zauna da Fatima wacce suke qira da Hajja a family house amma sai ya nuna ba haka ba shi yana son zuwa qaro ilimi, kakansa yayi-yayi ya zauna tunda anan Maidugurin ma suna da wadatattun makarantu amma yaqi dan haka sai suka bisu da fatan alkairi sannan ya tabbatar suna zuwa duba dangi, nan Alhaji muhammadu ya kamo hanyar Gombe tare da matar sa Hajja wacce har zuwa wannan lokaci bata taɓa ko ɓatan wata ba.

Sun shigo Gombe cike da sa’a inda basu staya ako wanni yanki na Gombe ba sai Ashaka, kasancewan yana da rufin asiri dan mahaifansa suna da qadarori kuma kamun ya taho ya buqaci wasu daga qadaran gadon sa kuma kakan sa baba-alhaji bai hana sa ba ya basa tunda garin mutane zai je ga kuma iyali.

Gida ya saya musu na rufin asiri, inda yake shiga cikin Gombe dan duba makarantar kaman yanda yayi niya, ya samu wani babban sangaya a nan cikin Gombe yana qara karatun sa in yayi kwana biyu a cikin Gombe ya dawo Ashaka yayi kwana biyu zuwa uku, a cikin wannan halin Allah yasa ya fara sana’ar fata inda Allah ya sawa abun albarka kuma ya karɓe sa, har dai ya siya fili a cikin Gombe.

Bayan dawowarsa Ashaka ya huta suna zaune tare da matarsa Hajja sai ya dube ta yace “Yah-gana na saya mana fili a Gombe saura ginawa in Allah ya yarda kinga sai mu koma can da zama abunmu, ke kin huta kewa na nima na huta kewanki da kuma jigile a hanya”.

Hajja sai tace masa “a gaskiya nikam Alhaji nafi son zaman nan garin sai dai in ka sayawa yaranka amma dai ni zaman nan yafi min”.

Ganin Hajja ta dage sai Alhaji muhammadu ya qyaleta ya cigaba da kaiwa da komowa tsakanin cikin Gombe da Ashaka, wanda ana cikin haka a shekarar su ta farko da zuwa garin Gombe kenan Allah ya azurta Hajja da samun juna biyu, wannan ciki ba qaramin farantawa Alhaji muhammadu rai ya yi ba, sosai yake kulawa da Hajja da abunda ke cikinta.

Tunda cikinta ya girma ta shiga watan haihuwan ta sai Alhaji ya kuma tunkaran ta da maganan komawa cikin Gombe amma nan ma taqi ganin haka sai yabar maganan gaba ɗaya shima ya daina yawaita zuwa Gombe dan ko harkan fata yanzu yana da yaran gida daga Gombe har nan Ashaka da sauran local government na Gombe har ma da wajen Gombe.

Ranar da naquda ya tashi wa Hajja ya ɗauke ta suka tafi asibiti, da zuwansu da haihuwanta duka bai fi minti biyar ba ta santalo yarinyar ta mace mai matuqar kyau dan tana kama da Alhaji kuma shi kyakkyawan gaske ne duk kyawun Hajja bata kama qafan sa ba, suka dawo gida da farinciki nan ƴan barka ke shigowa kowa ya shigo sai ya yabi kyau na yarinyar, ranar suna yarinya taci sunan mahaifiyar Alhaji wato Zainabu amma sai suka ɓoye sunan suna qiranta Yaanah, bayan suna da kwanaki dan har sun fita arba’in nan ciwo ya kama yarinya, ciwon ciki ba ji ba gani duk kyawun yarinya cikin kwanaki ta koma abun tausayi kuma a cikin wannan halin wani cikin ya qara bayyana a jikin Hajja nan dai abubuwa suka taru suka musu yawa sai gaba ɗaya ya ajiye shiga Gombe komai kawai ana masa yana daga gida yana kula da iyalan sa.

Yarinya taji sauqi inda zuwa yanzu take da kusan wata 7 cikin jikin Hajj na wata 6, kwastan suka wayi gari yarinya babu rai wannan rashin yarinya ya damu Hajja inda har ya janyo ta rasa cikin jikin ta, Alhaji yayi jimami na rashin cikin da kuma yarinyan amma ya miqawa Allah lamarin sa dan Allah ne mai bayarwa kuma shine mai karɓa.

Sai da Hajja ta shekara da yin ɓari sannan ta kuma samun wani cikin ta haifi yaranta ƴan biyu duka mata aka sawa ɗaya sunan Zainab ɗayan kuma sunan mahaifiyar Hajja wato Hajara, har yara suka kai shekara 2 Hajja bata kuma haihuwa ba inda ta masta ma Alhaji akan suje Maiduguri ba tare da ya mata musu ba ya miqa amanan ayyukan sa a hannun yaran gidan sa, suka wuce Maiduguri da ƴan biyun su inda suka isa lafiya kowa yayi farincikin ganin su stoho Alhaji-baba yayi ta sa musu albarka sannan yace su kula da bakin mutane akan yaran su, satin su biyu da zuwa zazzaɓi ya bugi ƴan biyu wanda ko lokaci bai ɗauka ba a ranan da Magrib zainabu tace ga garinku, an barta zuwa safe a mata sutura amma kamun gari ya waye itama Hajara tace ga garinku, Hajja tayi kuka har kaman zata bi yaranta dan sosai take qaunar ƴan biyun ta.

Sai da suka kwashe wata guda a Maiduguri kamun suka juyo garin Gombe, suna dawowa basu yi sati ba ciki ya bayyana jikin Hajja nan ta dinga addu’a da amfani da magungunan da baba-alhaji ya bata, wata tara ciff ta haifo yaronta namiji mai kama da ita inda ranan suna yaci sunan kakansa Nura, Alhaji sosai yake son wannan yaron nasa yana da shekara 2 ya ɗauke sa ya kaisa cikin Gombe yana karatun Alqur’ani a sangaya kuma yana zuwa boko, Hajja har da kukanta an rabata da yaronta qarami amma ko takan magananta Alhaji bai bi ba tunda ba zata zauna a cikin Gombe ba to shikuma yaransa za suyi karatu.

Ciki ne ya qara bayyana a jikin Hajja inda bayan wata tara ciff ta kuma haifo yara biyu mace da namiji, ranan suna mace aka sa mata maimuna takwarar matan baba-alhaji namijin kuma aka sa masa Mustapha, yara suna cika shekara biyu Alhaji ya ɗau Mustaphan ya kai cikin Gombe ya sanya shi a makarantar da yayan su Nura yake wanda shi Nura a lokacin shekarun sa huɗu 4.

Hajja haka ta zauna daga ita sai maimuna a Ashaka duk da Maimuna ma ba zaman gida take ba Alhaji ya sata a makaranta a nan cikin Ashaka.

Nura na da shekara goma ya sauqe Qur’ani mai girma kuma lokacin yana qoqarin shiga secondary, Mustapha ma a lokacin yana da shekaru 8 amma ya sauqe kuma yana qoqarin shiga junior secondary shima, Maimuna ta kusa sauqewa kuma itama tana qoqarin shiga junior secondary, Hajja bata sake haihuwa ba shi kuma Alhaji dukiya sai gaba-gaba yake dan zuwa lokacin filayen sa a cikin Gombe ba zasu irgu ba kuma tun bayan barowansu Maiduguri basu koma ba har yanzu da Nura ke neman shekara 11.

Nura ya kasance yaro ne mai sanyin hali da jin magana ga gudun zuciya, haka Maimuna akwai gudun zuciya ga ta shiru-shiru, saɓanin Mustapha da yake yaro mai hazaƙa fa qoqari amma yana da zuciya ga kuma kafiya, ba shi da reni amma ba ya storo kuma ba maganan kowa yake ji ba.

Maimuna na gama primary Alhaji ya ɗauko ta ya kawo cikin Gombe makarantar kwana ta fara secondary, Hajja ganin haka sai ta saduda ta yarda zata zauna cikin Gomben ita ma ganin za’a rabata da yaranta duka.

<< Jahilci Ko Al’ada 15Jahilci Ko Al’ada 17 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×