Hajja na dawowa cikin Gombe Alhaji ya sauyawa Maimuna makaranta daga na kwana zuwa na aje a dawo, Nura ma ya dawo gida amma shi Mustapha yaqi yace a makarantar zai zauna.
Rayuwa na tafiya abubuwa da yawa sun faru masu daɗi da marar daɗi inda a cikin wannan halin Allah yawa matar Alhaji-baba rasuwa inda saqon na riskar Alhaji ya tarkata iyalansa duka suka nufi Maiduguri cikin motan su na kansu dan yanzu Alhaji ba abinda bai mallaka ba,sun isa lafiya sai da suka share wata guda har da ɗori kamun suka juyo kasancewar. . .