A lokacin da Mujaheed ya yi hatsari, a wannan lokacin zuciyar Jawaheer ya buga da ƙarfi, ta dafe wurin tana Salati. Mom ɗinta ta riƙeta tana tambayarta lafiya? Cikin rikicewa ta dubi mahaifiyarta, ta ce "Na shiga uku Mom, wani abu ya sami Mujaheed, Mujaheed yana cikin matsala. Walh akwai abinda ya same shi, ki taimake ni Mom inje gare shi."
Kwantar da ita tayi a jikinta tana shafa bayanta. "Ki natsu kiyi masa addu'a, duka-duka yaushe ya rage ki zama mallakinsa? Ya kamata Jawaheer ki rage irin wannan zazzafar soyayyar da kike gwada wa akan Mujaheed. . .