"Yaushe kika zama malamar halayyar ɗan Adam Adda Halima? Asanina dai da ke, ke matar Sayyadi Ƙasim ce ban sani ba ko kin koma ..."
"Hafsa ba fa shirme na ke magana a kai ba. Ko ma ya nake kin sani ni ce mace mafi kusanci da ke, da kuma sanin halayyarki." Adda Halima ta faɗa tana matse fuska da kafe Hafsan da idanuwanta.
Murmushi Hafsa ta yi, sannan ta ɗauki hannun Adda Halima ta haɗe da nata tana matsawa "A cikin ko wata rayuwa ta ɗan Adam akwai sauye-sauye na warwarar zaren da ke cure ga labarinsa. . .