Da kallo kowa dake wajen ya bishi, zuciyar su ta riga data gama tsinkewa da tausayin sa.Wasu da yawa kuma suna jinjina butulci da rashin kirki irin na Hafsa, duk ɗiyar da zata yima mahaifinta haka to babu wanda ba zata yima fiye da haka ba.
Kallonta Ado yayi ya share hawayen dake Zuba akan fuskar sa, wanda babu makawa na tausayin Mahaifin nasu ne "Kiga yanda Alhajin mu yake kuka saboda ke Hafsa! Kiga hawayen takaicinki na sauƙa akan fuskar mahafinki daya zama tsani na kowani farin ciki arayuwar ki! Kinji haushin kanki Hafsa. Kin gayyaci she. . .