Shuru ne ya ratsa atsakanin su, ba tare da sun sake magana ba, sai dai har yanzu hannayen Adda Halima na riƙe dana Hafsat tana kuma kallon ta.
Zame hannunta Hafsa tayi ta kalli Adda Halima tana girgiza kai "Bazan iya cewa na sauya ba Adda Halima, kamar yanda bazan iya hararo abin da zai faru dani agobe ba. Tabbaci ɗaya nake dashi akaina shine zan iya miki biyayya kwatan-kwacin yadda ɗiya kema uwar ta."
Kallonta Adda Halima tayi, ta girgiza kai "Wanan ma bazan sameshi ba atare da ke ba Hafsa. Kawai zan iya kawar da kaina. . .