Ajiyar zuciya Hafsa ta sauƙe a lokacin da suka harba motarsu kan titi, tana jin gina da bayan kujerar motar. Tana kuma kintata adadin rashin kara na danginta, wadda a bayyane yake suna murna ne da tafiyarta.
Domin tana iya ganin shimfiɗaɗɗen murmushi a kan fuskar matan gidansu, kamar yadda take hango Asma'u amarya da take taka rawa tana juyawa.
Ita kanta Hafsa ta sani ta fitini rayuwar Amaryar Mahaifin nasu, wadda a zaman mako ɗayan da ta yi sai da ta hanata watayawa, da kuma kafa mata karan zuƙa akan yin girki da nama. . .