Hannunsa ya bi da kallo yana tuna adadin ƙonewar da ya yi, da kuma yankewar da ya yi, amma wai duk da haka Hafsat bata ga ba, sai cewa ta yi "Zai kashe ta?"
Dankalin ya ɗauka ya kai bakinsa, bai ji komi a tare da shi ba bayan garɗin da ke gare shi, ƙonewar da yayi bai rage shi da daɗinsa ba sai ma ƙara masa ƙamshi da ya yi.
Haka ya haɗa da yaga ƙwan ya kai bakinsa, shi ne ma dai babu ɗanɗanon komi a cikinsa amma kuma bai ji ƙarnin da zai. . .