"Wannan itace godiyar da zaki min? Ko kuma wannnan shine kalar naki santin? Ki dai ci a hankali, kada daɗinsa ya ɗebeki har ki ƙwarai." Ya gama maganar yana murmushi da lumshe mata idanuwansa.
Ɗago da kanta ta yi, tana kallonsa, ta sha jin ana cewa maza suna da saurin tashi da hassala idan mace ta kushe su, amma bata ga hakan ga Abdul-Mannan ba, domin shi ko alamun jin haushin kalamanta bai yi ba, balle ta samu wata ƙofar da zai nuna mata ta yi nasara akan sa.
"Kana so kace baka ji haushin abin da na. . .
Ma Sha Allah,