Skip to content
Part 1 of 9 in the Series Kaddarar So by Fatima Rabiu

Shimfida

Shin, wace k’addara ce za ta sa ‘yar uwa ta tsani ‘yar uwarta ta jini?

Shin, yaya za ka yi a lokacin da kika tsinci kanki a tarkon son wanda ‘yar uwarki take so.

Shin, me ya kamata ka yi a lokacin da wanda kake so yake gudunka?

Shin, wace k’addara ce za ta raba kan ‘yan uwa?

Shin, Kaddarar So za ta iya sawa d’an Adam ya aikata komai?

SURURE, LAGOS NIGERIA

Shekara ta 1995

“Mimi nahhh?”

Cewar wata matashiyar budurwa dake sakkowa daga kan matakalar bene.

Da gudu ta k’ara su inda Mimi take zaune, kiran da take kwala mata ne yasa, Mimi tashi tsaye.

Kallonta Mimi tayi ta ce “nikam Lalaah miye hakan? Kike ta kwala min kira fisbilillahi, baga ni ba ina zani”

Turo baki Lalaah tayi tana bubbuga k’afarta a shagwab’e, harda lauye kai ta ce “Mimi wani labari fa zan baki, zuwa na shopping na had’u da wan…K’asa k’arasa maganar tayi ganin kallon da Mimi ke jefa mata.

Can kuma Mimi tayi wani murmushinsu na manya, da sauri taja wo Lalaah a kusa da ita, ta zaunar da ita ta kalleta a tsanake.

Tukun ta ce “Lalaah ta, bani labari, hala an samomin siriki ne ba?”.

Kallon Mahaifiyarta Lalaah tayi, cike da d’unbin k’aunarta, domin Mimi irin iyayen nan ne, masu mugun sauk’i kai ga yaransu, idan tana tare da yaran nata kamar wasu jikokinkita haka suke tafiyar da rayuwarsu cike da farin ciki da kwanciyar hankali.

Sai dai kashhh wannan magana da Lalaah zata furta ma, Mimi ita, ita ce zata Yi sanadiyar da zata tarwatsa komai, da tasan da abunda zai biyo baya ko shopping d’in ma ba zata je ba, bare har suyi tozali dashi, kware shi su duka shine mafarin Kaddararsu Su, Arman Harum, sai dai kash sanin gaibo sai Allah. Kuma duk dabarar ka sai ka iske Kaddararka, a duk inda take.

Katse mata tunani Mimi tayi ta sake cewa.”i hear you Lalaah told me”

Turo baki Lalaah tayi ta sake shagwab’e fuskar nan tata mai d’auke da wani sahihin kyau, kai tsaye idan ka kalleta baza tab’a cewa nan take kyakkyawa ba ce, sai kayi mata kallon tsane ke da kyanciyar hankali, tukun zaka fahimci kyan nata bana tashin hankali bane.

“Mimi, guess who I saw while shopping today?”

“Well, I know, you told me, you are sad.”

“Sorry Mimi nahh, Mimi ai kinsan Doctor Arman Harun Maleek?”

“Ni ko nasan Doctor Arman Harun. koba shahararran likitan nan ba, wadda duk duniya tasan da zamansa, waye ba zai sansa ba, tunda ko ina ansha fira dashi a gidajen yad’a labarai na k’asar nan dama k’etare. But you are talking about him as if you met him before, to my knowledge you have never seen him physically because he’s not living in the country.”

Tab’e baki Lalaah tayi ta ce “No, Mimi, he did come to the country, haven’t you seen it in the news? And shopping d’in dana je ne, muka had’u dashi har mu kai magana, zaki yi mamakin shine ya kawo ni har k’ofar gida. People are so surprised that he talked and stayed with me. He’s very simple, on our way back, he stopped at intervals to greet and talk to the several women trying to talk to him. kin san Mimi hatta jami’an tsaron sun sha bala’in mamakin hakan da Ogansu har ya tsaya ya kula nima”

“I don’t understand, shi Arman Harun d’in ne, ya sauk’e ki k’ofar gidan nan? Don’t lie to me, Lalaah”

Tab’e baki tayi kamar zata fashe da kuka, ta ce “haba Mimi kin san bana miki k’arya Allah kuwa da gaske”

“Na shige su ke miya had’aki dashi harya miki magana, karfa kija azo ace za’a sace mu, yo ganinki da irin wa’innan masu arzik’in ai sai a d’iga ayar tabbaya akanmu, duk arzik’in Ubanku da kuke gani, ko kama k’afarsa baiyi ba, a hakan da ake ganinmu masu arzik’i, kinga Lalaah ki rufa mana asiri”.

Mimi ta idasa maganar tana waro ido waje, na tsananin mamakin Lalaah, yo taya ma za’ai ace taga wani Arman Harun wadda duk duniya ko ina ansan da zamansa, mutane attajirai kullum na turorowar zuwa ganinsa da sun zuwa asibitin da yake. but they don’t get to see him. That’s why they hear about him so much, when Lilaah, Lalaah’s sister, was working in the hospital at ARMAN HARUN’S HOSPITAL FAMILY’S, she was always in the middle of the day, she knew that she would also come back with his story.

“To ke Lalaah miye na farin cikin hakan, dan kawaii ya d’akko ki,”

“Hmm Mimi ni dai kawai na tsinci kaina da farin cikin hakan, ba wata magana mu kai dashi ba, hasali ba ko sunana bai tabbaya ba. We didn’t say anything to each other, in fact, he didn’t know my name, he just offered to help me when he saw me stranded looking for a vehicle, kin san ban fita da mota ta ba yau, tana wajan Lilaah. And me knowing who he was, I couldn’t refused.”

“Why do you still allow Lilaah uses your car? Wato ita taga tata, ta fara tsufa ta fara lalacewa, taki kuma sabowa baki je kika lalatata ba wajan iyayi irin nata, wato ita bari ta lalata takin yanzu, ke kuma da yake komai ta nuna tana so ko kina sonsa sai ki d’auka ki bar mata ko?”

Mimi ta fad’a rai a b’ace.

D’an rausayar da kai Lalaah tayi, cikin kwantar da kai dan kar aga laifin y’ar uwartata ta ce “a’a Mimi wallahi ba ita ta tambaya ba, ni ce na ga motar tata sai a hankali shine fa na bata tawa. Simply because she goes to work and I don’t.“.

“Ke ni rufe min baki, kowa ai da tasa baiwar, ke ba zane-zanen gini kike ba, wani lokacin ai ana d’aukar ki aikin kwangila wani kamfanin domin kije ki zana masu irin ginin da suke so, sai kuma ki ce baki zuwa aiki, kawai son kan Lilaah yayi yawa wallahi, ai duk Abbien ku ne shike d’aure mata gindi idan tayi wani abun”.

And what have I done?”

Cewar Lilaah, dake shigowa parlon, sanye take da doguwar abar y’ar Dubai dake jikinta sai kuma farar rigar doctor’s dake saman rigar, rik’e take da jaka dake cike da takardu na aiki, sai d’ayan hannunta dake rik’e da key na mota. Can kuma saita d’an ya mutse baki, tana binsu da kallo. D’an dakatawa tayi jin muryar, Mimi dake kiranta a zafafe. Domin tunda tayi magana ta farko na cewa, miye tayi, kawai tana idasa k’arasowa ta fara hayewa sama, inda d’akinsu yake, domin a gajiye take lik’is, ga b’acin rai na Doctor Arman data kwaso, a yau d’in. Tayi dana sanin zuwa gidansu Doctor Arman, duk Bilkees ce tasa ta zuwa, wai taje domin ta gaisar da Mahaifiyarsa. Kware Mahaifiyarsa wacce suka ji ake kira da, My love a gidan, sun samu tarba ta mutumci, Bilkees y’ar uwarsa ce wacce suke Uba d’aya da Arman ita doctor ce, jininsu ya had’u da doctor Lilaah domin zan iya cewa, halayya yazo d’aya. They all are vey proud and arrogant and are lucky they’re wealthy enough to show it. Zuwan da su kai, sunyi tozali da Ya Arman wadda zasu fito shi kuma zai shiga gidan, Bilkees ta fito domin raka Lilaah wajan motar ta sukai kicib’os. Ta gaida sa sarai yaji, amma yayi k’unnan uwar shegu da ita. Daidai gwargwado ta shak’a, yarfin da yayi mata, domin ita macece marar son raini, amma tasan ita ta Siyama kanta rainin tunda ta nuna tana mahaukacin sonsa, kuma ya sani. Shine yake wulakantata. Sai Bilkees ce keta bata baki, kan cewa, ta kwantar da hankalinta insha Allahu Ya Arman ita ce zai aura. Wannan abunne kawai da Bilkees ta ce mata ya sanyaya mata zuciya.

Katse mata tunani Mimi ta sake yi k’aro na biyu, tana kallonta cike da takaici ta ce “wai ke Lilaah yaushe zaki canza wannan halin naki, na rashin sallama, idan zaki shigo ma mutane gida? Kuma kin shigo kin iske mutane bak’o gaisuwa, haka na koyar dake?”

K’aro na barkatai taja d’an k’aramin tsaki yadda Mimi ba zata ji ba, domin ko banza suna tsoron Mimi duk da wasan da take yi dasu hakan baisa taja sun raina ta ba. kai hatta Abbie suna shakkarsa sai dai kuma banda Lilaah, domin shike nuna yafi ji da Lilaah komi take so kota tabbaya kai tsaye yake bata, abunda Lalaah bata yi kenan, yawan tabbayarsa abu, domin ita tana samun kud’i sosai wadda harya d’ara albashin Lilaah, komai dasu take yi, hatta motar ta da Lilaah ke hawa yanzu ita ce ta sake ma kanta, mai tsadar gaske, wadda ba k’aramin tashin hankali ake ba a gidan, a ranar da Lalaah ta sayi motar, sai da Mimi ta nuna b’acin ranta tukun, da Abbie so yayi ya amsheta su duka su zauna babu, sai da Mimi ta nuna sam bata lamunce ba, ta kuma tuna mai da cewa, “ka manta Abbie Lilaah mota nawa ka sake mata ba tare da ka saima Lalaah, tun wacce ka sai masu tare, baka sake sai mata wata motar ba, bayanta ka sake ma Lilaah mota ta kai uku, amma Lalaah bata tab’a d’aga kai ta ce danmi ba, sai yanzu ta samu na kanta ta saya kuma za’a ce baza tai anfani da ita ba, ina ganin hakan ba adalci bane, gaskiya abar mata motarta ta hau”. Bai sake maganar motar ba, amma Lilaah ta matsa mai kan cewa, itama fa sai ya sake sai mata mota, wacce tafi ta Lalaah kyau da tsada, dole ya rarrasheta, aka sake mata sabuwar mota wacce tafi ta Lalar, sai dai ba’a je ko ina ba, ta lalata motar. Ta Lalaah kuma tana nan, ganin hakan yasa ta aje tatan take arar ta Lalaah domin fita kunya, dan ita ta tsani, seeing her seen is not enough, ko bata kai ba, tafi son taga tafi kowa haka take so, ita haka take ganin shine dai-dai.

Jin muryar tayi tsakiyar kanta, wata iska taji ta gifta mata, kamar tafin hannun mutum ta gani, sai kuma taga an rik’e hannun, da hanzari ta d’ago tana duban Mimi, data d’aga hannu zata sharara mata mari, da sauri kuma Lalaah ta k’araso wajan, ta rik’e hannun Mimi, tana zare ido.

“Please Mimi, I’m sorry, I think she didn’t hear what you were saying, and kinga yana yin data shigo kamar bata cikin hankalinta fa”.

Lalaah ta idasa maganar tana sakin hannun Mimi da ranta yake a b’ace

Wani kallon tsananin takaici Mimi ke aikama Lilaah ta ce “wato kin maida ni y’ar iska, tun d’azo nake b’ab’aton zance amma kinyi shuru kin kyale ni, yau ga y’ar iska na magana, kuma sa’arki ba?”

Ba ta ce komai ba, sai Mimince ta sake cewa “ai kina jina, mi yasa kika d’au motar Lalaah kika fita da ita, shekaran jiya ba munyi dake zaki ba, Yayanku Aliyu idan ya dawo daga Abuja ba, aje ya tabbayi Abbie ya basa kud’in gyaran motarki a gyara kici gaba da hawan motarki, ki kyale mata tata ba. Didn’t talk about that?”

Lilaah da wani bak’in ciki da hassadar y’ar uwarta ya kamata, wato zama tayi tana zuga Mimi, domin idan ta dawo gida ta k’ara tsanarta akan wacce take yi.

“Tambayarki nake kin tsare ni da ido”

K’asa tayi da kanta, jin wani abu wai shi kunya an dizgata danmi za’a mata fad’a gaban K’anwarta, akan wata aba mota, kai ita ce ma ta zubar da darajarta. Why did she borrow it?.

Mimi, how can I call Abbie to request something from him while he’s not in the country? And that’s why I couldn’t call Ya Aliyu too.”

Lilaah ta idasa maganar tana duban Mimi

“Eh ba shakka, yau kika san da hakan, da da kike kiran nasa yana can fa idan kina son abu, ki dame sa da kira da naci harsai ya baki koya turo miki, sai yanzu da ba kiyi niyya ba iyee?”

Wani abu ne ya tsaya mata a wuya, har bata san sadda ta ce “ni dai Mimi indai mota ce ga abarta can bazan sake hawa ba, shikenan?”

“Da dai yafi miki, dama za ki yi zuciyar hakan”

Cewar Mimi tana komawa ta zauna akan kujerun parlon.

Wani kallo Lilaah ta watsama Lalaah, ta juya ta haye sama. Da sauri Lalaah tabi bayan y’ar uwar tata, domin Allah ya sani bata son b’acin ran y’ar uwar tata.

Kaddarar So 2 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×