*****
Jawaheer tana nan kwance a sume, tuni numfashin Ummi ya ɗauke itama ta zube anan. Hakan yasa wurin ya sake rikicewa da koke-koke. Alhaji ya ƙara so gaban Farouk ya taɓa shi, ya sake ja da baya yana jin gabansa yana tsananta faɗiwa. Shi kansa yasan idan babu Farouk rayuwarsa za ta ci gaba da yi masa barazana ne, har shi ma ya amsa kiran Mahalicci. A hankali ya zaro wayarsa ya danna lambar Likitansu ya sanar da shi komai. Cikin gaggawa likitan ya iso, cike da saƙe-saƙe.
Anti Laila har muryarta ta dashe. . .