Washegari suka tafi, Umaimah ta bar Kauthar cikin zuzzurfan tunanin maganganun da tayi mata.
Sai a lokacin da suka je wajen aiki ne ta fahimci lallai zancen Umaimah akwai kamshin gaskiya a tattare da shi. Matan ofishin tun daga kan musulmai da kiristoci, suna ta karakaina da zarya a sashen nasu duk akan dalilan da basu taka kara sun karya ba, sai su fake da sunan aiki.
Duk kuwa da yadda shi gogan ya nuna kamar ma hakan bai dameshi ba sam, kuma bai lura da manufarsu zuwa gareshi ba, hakan bai sanyaya ran Kauthar ba ko kadan.
Da ta. . .