Ya ce yanzu ina amfanin abinda tace da Safiyyah a matsayinta na babba mai hankali kuma Uwa agaresu wadda ta san cewa in’ina halitta ce ta Allah?
Baba ya furzar da numfashi cikin bacin rai, ya dubi Mama yace “Annabin Allah ma yayi in’ina (Musa Alaihissalam) na tabbata kinsan hakan a tarihin Annabi Musa.
Tashin farko a haduwarku ta farko kin zubar da girmanki ga surukarki, matar tilon danki. Wannan cin fuska ne kikayima danki ba ita ba, tunda shi kika bari da ji miki kunyar”.
Mama zancen ya fara isarta, ta shuno baki gaba, tana son cewa. . .