Ruƙo hannunta Khamis ya yi a lokacin da take yunƙurin sauka daga kan gadon, cikin dagewa akan son fahimtar da ita ya ce, "Aisha don Allah ki saurare ni, wallahi ko kusa ban faɗa miki haka don in wulaƙanta ki ba, kuma..."
"Na ce ka sake min hannu."
Ta faɗa tare da fizge hannunta.
Direwa ta yi daga kan gadon sannan ta ɗora da,
"Kuma wacce magana ce zan ji daga bakinka? Bayan ka tabbatar min da butulcinku na 'ya'ya maza. A baya har cewa kake idan akwai matan aljanna a duniya to ina. . .