Zuzee na jin Aisha ta ce Khamis ya kusa dawowa ta yi saurin faɗin, "Eh a bari sai jibi ma, ko wani lokacin kafin ta dawo dai."
Tana rufe baki ta shiga haramar tafiya a ƙasan ranta saboda bata so Khamis ya iske ta a gidan.
Aisha da ta ƙagu ta ga me ke cikin ɗakin Maryam ta ce,
"Goben dai don Allah."
Don rabon ta da ɗakin tun ranar walima da ta raka Khamis.
Ɗan jim kaɗan Zuzee ta yi, daga bisani ta ce,
"Gaskiya gobe ba zai yiwu ba, ni tsoro nake kada muna cikin bu. . .