Saboda tsabar kiɗima da Jummai ta yi sakamakon jin labarin mutuwar mahaifinsu, sai ga tsohon cikin da ta daɗe tana ɓoyo a fili mutane suna gani.
Kwata-kwata ta kasa yadda da cewar ya mutu, domin a yadda suka baro shi, ko kusa ba alamun tsanantar ciwo a tare da shi.
Kuka sosai ta riƙa yi tana faɗin "Wallahi ƙarya ne, babanmu yana nan da ransa bai mutu ba."
Wannan kukan shi ya ƙara jawo taruwar mutane a ƙofar gidan, wanda dama wasu tuni sun hallara saboda jimamin mutuwar Malam Amadu. Haƙuri wasu suka ri. . .