Fuskar Jummai cike da mamaki da kuma tsoro ta dube shi, don bata taɓa tsammanin haka daga gare shi ba.
Sassauta murya ta yi sannan ta ce, "Ashe dama haka kake, gaskiya ka bani mamaki, kuma yanzu na tabbatar da taimakon da ka ke mana ba don Allah ka ke yi ba."
Murmushi kawai ya yi, saboda ya san bai taɓa taimakon wani don wata manufa ba face domin Allah. Asali ma ko da dukiyar haram baya sadaka sai da wadda ya san da guminsa ne ya same ta, ya zaɓi haka ne domin neman gafarar mahaliccinsa. . .