Su Humaira na wanzuwa cikin makarantar, ta rufe Binta da fada ta inda ta shiga ba ta nan take fita ba, akan me Bintar za ta karbi kudin aikin da Sadik ya dawo musu da shi?
Cikin sanyin murya Binta ta ce: “Don Allah ki saurara mana, me yasa kike haka ne? Mutumin nan fa ba yaro bane irin shashashan nan, da ganinsa ya san me yake yi ba shiririta bace a ransa. Sannan kuma ki duba shi ma fa malami a wannan makaranta, bai kamata ki yi masa irin wannan ba tunda har ya fesar miki da abin da. . .