Skip to content
Part 20 of 23 in the Series Ƙuda Ba Ka Haram by Sadik Abubakar

BAYAN SATI BIYU

Bayan kamar sati biyu da zuwan Usman makarantar su Humaira, sai ya sake dawowa; amma a wannan karon ba wajen Humairar ya zo ba, ba da ita yake muradin haduwa ba. Saboda haka ma ko sanar da ita bai yi ba, gaba-gadi kawai ya niki gari ya tafi. So yake ya hadu da Binta ko Ruky; tun da ya gan su maitarsa da arwarsa suka doru akansu. Ya so tun a ranar ya samu lambar wayoyinsu, musamman Ruky dayake ganin da alama ‘yar hannu ce ta san komai, ba za a sha wahala ba za ta ba da kai; domin ya lura kanta na dan rawa musamman idan ta ga kudi.

Cikin sa’a kuwa yana shigowa bakin kofar makarantar kafin ya kai neman wajen tsayawa, Ruky ta kawo kai za ta fita, kwatsam sai ya hange ta cikin ransa ya ce “Faduwa ta zo daidai da zama.” Amsakuwwar motar ta danna; kamar ta san da ita yake, sai ta dubi inda ta ji sautin amsakuwwar yana fitowa daidai lokacin shi kuma yana dauke gilashin sashen da za su iya hada ido. Ai kuwa karaf suka yi ido hudu da juna, murmushi hade da sigina ya sakar mata; ba tare da ya kira ta ba kai tsaye ta nufi wajensa tana sakin nata murmushin yayin da shi kuma ya dan saki hanya ya gyara parking. Tana isa jikin motar kafin ta yi magana ya ce,

“Am sorry ‘yammata, na dakatar dake daga uzurinki ko?”

“No ba damuwa; ni kamar ma na so na shai da wannan fuskar?”

Cikin sigar kwarkwasa da yaudara take wannan maganar, Usman ya dan lumshe idanu ya bude sannan ya ce, “May be haka ne, there was a time da na taba shigowa school din wajen wata yarinya kamar ma friend dinki ce.”

“Okay, tabbas na tuna Humaira ko? Ai tana ciki. Bari na kirawo maka ita.”

“No,kyale ta kawai ai ba wajenta na zo ba yanzu.”

Cike da mamaki ta dube shi ta ce,“Ba wajenta ka zo bayan? Is she not your girlfriend? To wajen wa ka zo kenan? Na san dai you’re not part of the students.”

Kashe mata ido ya yi hade da yin wani tsinanen murmushin yaudara sannan ya ce,“I have already saw the one I need to meet.”

“Hmm! Wai ba shigowarka ba kenan, na ga ko ciki ma ba ka karasa ba amma kuma ka ce har ka hadu da wanda kake son gani?”

“Yeah! Dama fa ni wajenki na zo kuma sai ga shi am so lucky ban sha wahala ba na hadu da ke.”

Wani irin murmushin ‘yan bariki ta yi masa sannan ta ce, “Wajena kuma? Dama mutum ya taba zuwa wajen wanda bai sani ba? In fact, ba shi ma da tabbas din zai hadu da shi?”

“Hmm! Ba ki ji statement dina na farko ba, na ce am so lucky; ni dan sa’a ne, shi yasa tun da farko da na gan ki na tabbatar na yi sa’ar.”

Ta yi sake yin murmushi tare da cewa, “You’re talking in the language that I didn’t understand. Wai Humaira ba budurwarka ba ce? Ni fa kawarta ce kuma ka ce ka zo wajena ba ma wajenta ba.”

“Come on baby, why are you behaving like a kid? Yanzu dai ina za ki?”

“Mun fito daga lakca ne shi ne zan dan fita waje na huta kafin next lecture.”

“Well, ko za ki dan shigo sai mu juya mu fita tare?”

Babu musu ta ja kofar motar ta shiga, Usman ya yi cikin makarantar domin ya samu sararin da zai juyo motar su fice, daidai lokacin da yake kokarin nade steering zai juya karar idanuwan Humaira akan motar bangaren me zaman banza, wato inda Ruky take zaune, nan take ta gane motar Usman ce, kuma Ruky ce wannan shi din ma ta gane shi. Gabadaya ta zama kurma, bakinta ya yi matukar yin nauyi; ta gaza cewa komai har ya juya suka fice daga makarantar.

Mutuwar tsaye Humaira ta yi a wajen tana ci gaba da kallon kofar tamkar me duba jinjirin wata; kusan mintuna uku tana bin hanyar da kallon, yayin da tuni zuciyarta ta fara kitsa mata tunane-tunane kala-kala. Dayake tare da Binta suke, fitowarsu kenan daga lakca ba su kai ga rabuwar ba, sai Bintar ta ce,

“Wai lafiya kuwa? Me kike ta kallo ne a waje daya har bacin rai na neman bayyana a fuskarki? Ko ba ki da lafiya ne?”

Wadannan jerin tambayoyin da Binta ta jera mata ne suka saito da hankalinta, dayake gwana ce wajen shirya karya da zancen kare kai, sai ta ce,  “E wallahi kaina ne na ji yana dan sara mini kadan; shi ne na yi addu’a.”

“Assha! Sannu fa, to ko za mu je ki karbi magani a clinic ki sha?”

“No, ba ma sai na karba na, zai daina Insha Allah.”

To shi kuwa Usman yana ficewa da Ruky daga makarantar ya ce da ita, “Ina kike so mu je yanzu ki huta din, sai ma mu dan sha ice cream ko?”

Ko gezau ba ta yi, sam babu alamar tsoro ko firgici na rashin sanin ko shi waye? Ta fahimci bukatarsa ,don haka hankalinta kwance ta ce masa, “I don’t know anywhere in Kano; karatu ne ya kawo ni kuma a hostel nake camping.”

Karya ce tsagwaranta ta shirga, babu inda ba ta sani ba a Kano, duk da cewa ba ‘yar garin ba ce, amma ko ‘yan garin ba su kai ta sanin irin wuraren shakatawa da hotel-hotel ba. Kai hasalima bai fi satinta na farko a Kano ba ne ta kwana a hostel din makaranta. Da marece wajen Magariba ko bayan Magaribar, motoci kan rika fakawa a daura da kofar makarantar sai dai ka rika ganin yarinya ta fito ta bude mota ta shige an yi gaba da ita. Ruky da Ire-iren ta masu kwadayi da rashin kamun kai haka suke yi.

Murna da farinciki ne suka mamaye zuciyar Usman, wato ya yi sabon kamu; yau zai bare gyadarsa sosai. Bisa yadda ya yake ganin alamu babu shakka Ruky za ta ba shi hadin kai; Kings Hotel na cikin Sabon Gari ya nufa da ita. Ya yi parking suka shiga reception ya biya kudin daki  VIP, sannan suka wuce, dakin yana can saman benen hotel din. Daki mai lamba 15, ya bude suka shige ya dube ta ya ce, “Ruky baby!”

Sunkuyar da kanta ta yi hade da sakin murmushi me dan sauti sannan ta ce, “Where do you knew my name?”

Dariya ya yi sannan ya ce, “Okay, ashe ma kin manta, ke ce da bakinki kika fada mini since that day. Kin san abin da kake so dole ne ka zama mai kula a kansa.”

Zama ta yi a bakin gado, shi kuwa sai ya fara kokarin rage kayan jikinsa, bayan ya cire ya yi oda aka a kawo musu drinks da dan abin ciye-ciye sannan ya shiga toilet domin ya dan sanyaya jikinsa. Kafin ya fito tuni waiter ta kawo musu abin da ya bukata, yana fitowa ya iske Ruky ma ta cire dan karamin hijabin nan da ke tsayawa iya wuya, wanda ake kira da a tsokani Shari’a, ta kishingida a kan gadon. Idonsa kyar akan kirjinta, wata matsiyaciyar riga ce a jikinta irin me fafakakken wuyan nan, wacce idan mace ba ta iya sawa ba sai kafadarta daya ta rika fitowa. Abubuwan nan na kirji ya gani tunjima-tinjima sun cika mata kirjin sosai, sun yi mata hani’an ga su kuma a tsaitsaye. Ita dai ba wata me kiba ba ce sosai, amma tubarakAllah! Tana da duniyar Fulani. Nan da nan idanuwan gogan naku suka fara kadawa zuwa launin ja, yayin da tuni feelings dinsa ya fara reaction.

Hakika Ruky, kyakkyawar yarinya ce ta kowacce fuska sai guri daya da ta samu cikas, wato babu kyawun tarbiyya. Tana da kyawun sura, fara ce irin farin nan me ban sha’awa; tana da doguwar fuska da idanu da hanci da baki madaidaia. Tsayinta matsakaici ne, tana hips ba irin sosai din nan ba wanda ya dace da yayin kibar jikinta, mazaunanta ba irin round din nan ba ne gabadaya, sun dan taso suna da tudu; shape dinsu na fitowa sosai musamman idan ta saka wandon da ya matse ta.

Gefen gadon Usman ya zauna ya ce, “Ya ya na ga ba ki taba komai ba kin kwanta?”

Murmushi ta yi sannan ta ce, “Kai nake jira ai.”

Dariya ya yi tare da cewa, “Okay, na manta fa ashe ni ya kamata na ba ki a baki.”

Yana fada ya bude plate din; wani farfesun kifi ne irin karfasan nan manya, ya gutsira ya kai mata baki, sai ta dan sunkuyar da kanta alamar wai ita mai kunya ce. Rungumo ta ya yi tare da cewa, “Come-on dear! Ki karba mana.” Ya sake kai mata daidai kofar bakinta, ta dan bude kadan ya saka mata, ta rike da hakoran gaba. Daya hannunsa kuma yana bayanta, Ya shafi bayan nata da shi tun daga wuyanta har zuwa mazaunanta; ya dan latsa mazaunan ya ji su dumurmur alamun ba sosai ake kwanciya da ita ba ko kuma tana kula da jikinta ne. Ya kama gefen pant dinta daga jikin kugunta ya ja sannan ya saki, robar pant din ta dan yi irin karar nan ɗas.

Zuciyar Ruky ko shaking ba ta yi ba, babu wata alamar razani ko tsoro, ce mata ya yi, “Ki ci wannan abincin fa, ni a koshe nake dama saboda ke na sa a kawo.”

A hankali ta rika cin kifin nan tana shan lemon, dama yunwa take ji sosai dalilin da ya fito da ita kenan domin ta dan samu ko biscuits ne da lemo ta ci; kiwa ta hana ta tsayawa ta ta girka abinci. Haka ta cika cikinta fal!

Ita kuwa Humaira abin duniya duk ya ishe ta, Binta ta ce, “Ya ya kan naki? Da fatan ya lafa?”

Humaira ta dan yatsina fuska tare da cewa, “Da sauki, na gode. Ba za ki je wajen Sadik ba ne? Watakila akwai aikin da za ki rage musu.”

“Aa ai ba na tafi na bar ki ba ke kadai alhali ba lafiya gare ki ba.”

“Ai ni na ce miki ki je tunda kina taya shi aiki; babu mamaki akwai wani aikin da za ki yi masa, ki je kawai ba komai na gode.”

Humaira ta matsa akan lallai sai Binta ta tafi domin ta samu damar kiran Usman, ko za ta tabbatar da shi din ta gani ko kuwa dai gizo ya yi mata? “Kai babu ma wani maganar gizo, Usman ne kuma wacce na na gani zaune cikin motar Ruky ce.”

A zuciyarta ta yi sanny maganar, da Binta ta lura cewa Humaira ta fi son ta tafi din ta kyale ta ita kadai, sai ta yi tafiyarta café din ta bar ta a wajen. Bacewarta keda wuya, Humaira ta zaro waya ta kira Usman, daidai lokacin ya fara romancing din Ruky; mika hannu ya yi ya dauki wayar yana kallon screen din idonsa ya yi tozali da lambar Humaira, dagawa ya yi tare da cewa, “Hello ranki yadade, da fatan tashi lafiya ya gidan ya karatu?”

Ta amsa masa da, “Lafiya kalau, karatu Alhamdulillah!”

“Ya ya aka yi ne?”

Ya tambaya yayin da yake ci gaba da shafa jikin Ruky. Humaira ta ja numfashi tare da cewa, “Lafiya kalau, dama yanzun nan babu jimawa na ga wata mota ta fita daga makarantarmu kamar taka; shi ne na ce bari na kira ka na ji kai ne ka shigo amma ba ka neme ni ba mun gaisa?”

Marar gaskiya ko a ruwa gumi yake, nan take sai ya kama in-ina harshensa na sarkewa ya ce, “E ni, a, a’a, a ba ni ba ne; ba ni ba ne wallahi sai dai ko irin motar ce kika gani. ”

Ruky da ke kwance a kirjinsa ta yi luf da ita tamkar ta samu kirjin mijinta na sunna ,wani irin fitinannen nishi ta saki wanda hatta Humaira sai da ta jiyo shi. Dama ta yi nishin ne da biyu, domin wacce suke waya da Usman din ta jiyo duk da cewar ba ta san kowace ce ba; amma dai ta san duk kanwar ja ce. kin wannan nishi ya kara tunzura hankalin Humaira, wani zazzafan radadi ta ji yana kewaya mata zuciya, kamar ana caccaka mata allura. A lokaci guda kuma muryarta ta yi sanyi ta ce, “To don Allah yanzu a ina kake? Kana gida ne?”

Wannan tambayar da ta yi masa ma sai ya sake dabarbarcewa, “E,  a yanzu ina, a’a ba na gida; kin gane dan ba ni lokaci kadan zan kira ki.

Yana fada bai jira jin me za ta sake cewa ba ya kashe wayar. Hakan ya kara tayar mata da hankali matuka; tunani me zurfi ta afka wanda a ciki ta fi karkata ga zargin cewa mutumin nata dai tare da mace yake. Domin yanayin da yake ba ta amsa da nishin macen da ta ji  da kuma shirun da wajen yake da shi ya tabbatar mata irin wajen da suke kebewa ita da shi ne.

“Dama ashe haka yaya Usman yake? Neman mata yake yi? Ashe ba ni kadai yake kulawa ba? Ai ko daga yau ba ni babu shi; ba zan sake yarda da shi ba.”

Maganar da Humaira take da zuciyarta kenan kafin ta yanke shawarar kiran wacce take zargin ta gani sun fita tare da Usman din, wato Ruky. Kiran wayarta ta yi daidai lokacin Usman ya haye kugunta, babu abin da take iya ji bare ganewa; ihu kawai take shi kuwa ya kuke sai sha’aninsa yake yi. Yana jin wayar tana ruri amma ko kallon wajen da take bai yi ba, haka ta yi rurinta ta yanke. Humaira ta sake kiran wayar, da ya ji karar na neman takura masa sai ya dauki wayar ya katse kiran; duk da haka Humaira ba ta hakura ba, sai ta sake danno wani kiran, to a wannan karon da ya dauki wayar sai ya kashe ta gabadaya ma. Sake kiran da Humaira za ta yi sai ta ji wayar a kashe dif! Kifa kanta ta yi tana cizon lebe.

<< Kuda Ba Ka Haram 19Kuda Ba Ka Haram 21 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×