Wani irin wulakantaccen kallo Humaira ta bi Binta da shi sannan ta ce, “Allah Ya jarabce shi da son mu ko dai Ya jarabce shi da so na? Ke ai ba son ki yake ba, ke ce dai kike ta cusa kai kina masa tallar kanki amma sam ba ya son ki, ni yake so. Don haka ki gyara lafazin bakinki malama.”
“Hmm! To Alhamdulillah! Na ji aje a hakan, ni dai na san yaya Sadik ko a mafarki ba zai ce ba ya so na ba. Domin ba a fi ni zannuwa ba, to ba za a baɗa. . .