To wadannan mutane guda biyu wato Anty Zara'u da Malam Sadik, abokan aikin Anty Sakina su kadai ne take dan fadawa matsalarta su taushi kirjinta ta samu sauki a ranta. Sun zama aminanta, ta su ta zo daya, su ukun nan tamkar 'yan uwan jini suke. Haka suke mu'amalarsu duk abin da ya samu daya to tamkar su ukun ya samu, sawa'un abin farin ciki ne ko kuma akasin hakan ne. Sukan hadu su yi duk me yiyuwa idan wata damuwa ta samu daya su samar da mafita ko kuma aƙalla su rage wa wanda abin. . .