Daidai lokacin Alhaji Aminu ya turo kofa, duk warin giya ya cika dakin, ga dansa kwance cikin jini yana faman amai. A sukwane ya karasa gare shi ya janyo shi kan cinya yana jijjiga shi. Sunan Nurat kawai yake faman kira, a rude ya kira likitansa a waya tare da yi mishi bayanin abin da ke faruwa.
“Zaruk ashe karya ka yi min, da man yaudara ta ka yi ka ce ka daina? Me ya sa?”
Kokarin kwacewa ya dinga yi daga jikinsa yana kiran sunan Nurat.
Kuka Alhaji Aminu ya saka, yadda ya ga jini ya tsananta zuba. . .