*****
“Ya aka yi haka ta faru? Ta ya ya?”
Ya dago kai, maganarshi da kyar ta ke fita.
“Wacce nake matukar kauna, wadda sonta ya zame min tamkar ciwo da wadda nake matukar kauna, na shaku da ita, wadda ita kadai nake ganin mutunci, wadda nake jin dukka dabi’unta babu na yadawa, wadda na yi hakurin zan je gare ta ko da bana sonta zan iya aurenta don kwadayin halayenta, sai ga shi ita ce ta dunkule ta zamo abu daya, ita ce! Ita ce ke kokarin kyautar da zuciyarta. Salim na rasa ya zan yi? Ta lalata komai. . .