“Ya Allah wai ke wace iri ce ? kinsan yadda deedat ke da tsafta, idan kinayin kwaskwarima agida kifita aksa ganewa, to yanzu nan makwanci zaku hada, idan ya kusance ki zai dinga jin bashi”.
“Oh mom, kinsan bana son sanyi, bana son wanka akwai wahala, inaga in nawanke hammata ba zai gane ba”
“Shikenan yanzu tashi kishirya sai ki tafi can gurinsa”.
Kamar yadda ta ambata haka tayi wato tsaka tsami ta wanke hammata, da kafafu, ta sheka uban kwalliya kai sai ka zaci wanka ta sheka, riga pitet ta saka da dan gajeran siket, mazaunanta a shafe tumbi ya. . .