Skip to content
Part 21 of 24 in the Series Kyautar Zuciya by Bilkisu H. Muhammad

Motsin tahowar Aazeen suka ji ya mike ya koma kan kujera.

‘Ka tabbatar da taurin kanta ko?”

“A’a yanzu ki sa a kawo mata abinci za ta ci”.

Ta dubi Nurat, “Wai haka?”

Ta jinjina kai.

“Lallai ka ciri tuta”.

Ladidi ta kwala wa kira. A sukwane ta shigo ta durkusa.

“Ke me za mu samu a gidan?”

“Rangida kin sani yau ba a yi girki ba, amma za a samu cake ne kawai”.

“Oky za ki iya kawo mana, maza yi sauri”.

Ladidi ta tashi ta fita. Ba a fi mintina biyar ba ta shigo rike da filet. Aazeen ta karba ta ajiye a gaban Nurat. Cikin muryar lallashi.

“Kanwata kin yi min alkawarin za ki ci abinci, maza ki ci, kin ji”.

Tsintar kanta ta yi da soma ci, ya kasa janye ianu daga kanta har sai da ta kware. Da sauri ya mika mata ruwa, hakan da yake I yana kara sonsa a zuciyar Aazeen, ta tabbata mutum ne mai kula, ya nuna wa kanwarta kulawa ina ga idan ita ce? Murmushi ta dinga yi.

“Adam na gode, rashin cin abincinta ya tayar da hankalin kowa, musamman Dad. Mun gode sosai”.

Kallonta Nurat ke yi cike da mamaki, ba ta taba jin ran da Yayarta ta furta kalmar godiya ga wani bare ba, ta kara karaya sosai hakan na tabbatar ma ta yadda Aazeen ke kaunar Admu.

“Ina son gobe zan yi asubanci zan koma garin mu”.

Rab gaban Nurat ya fadi, dan kwana biyun da yayi shakuwar su ta karu, duk kuwa da rashin jituwar da ke tsakaninsu, cikin dubansa Aazeen ta numfasa.

“Ta yaya za ka tafi bacin gaga rumin bikin da ke gaban mu?”.

“Kada ki da mu ba rana ita yau ba ne,? kwana shida zan yi na dawo”

Ta ji dadin kalamansa.

“Kaga a wannan zuwan ne zan gabatar da a kai, gurin Daddy na san zan yi farin ciki”.

*** *** ***

ABUJA

Cikin sautin dariyar Kabir da Nabila ta cika sitroom din.

“Ka bari tunda ban iya ci ba, mu sai mu yi ta ci, da ma Ummi ce ke take min burki, amma yanzu ga ki ke ce uwardakina, ke ce tsanina, na san duka burikana za su cika”.

Kanta ya kara fasuwa.

“Kada ka damu K.B, abu daya zan yi, zan jajirce a kan Yaya Deedat sai ya dora ka a kan takara ko da na dan majalissa ne”.

Ya ko gyara zamansa.

“Wayyo Hajiya ta, kin sosa min inda ka ke yi min kaikayi, wannan shi ne mafarkina, za mu fantama ke nan. Na dade ina yi wa Ummina maganar amma ta ki ba ni hadin kai. Kai na gode wa Allah da ki ka zamo matar Deedat, yanzu labari zai sauya Hajiyata, daga ke babu kari, babu wadda za ta sha gabanki muddin muna raye’.

“Ka bari ita ma Ummi zan nusar da ita, za ma ta amince da batunmu, ni kaina ba don mutumin naka na da tsauri ba, sai na tsaya takara”.

Ya yi dariya.

“Ke dai ki fara tura ni idan ki ka cicciba ni komai sai ya biyo baya, amma fa sai kin rage tsoron nan na ga kina shakkarsa sosai’.

“Abin a jininsa yake kai ma ka sani”.

“Na ji Aisha shiru”.

Nabila ta ce, “Ina ji Ummi ta tsare ta da hira”.

Ba ta gama rufe baki ba ta shigo.

“Tunda ga ta ni zan wuce, sai na dawo daukata bayan sallar magriba”.

Yana ficewa Aisha ta dubi Nabila.

“Na ga gida duk ya yamushe kamar ba gidan amarya ba, ko har an gama amarcin ne?”

“Haba Aisha, ba ki yarda da abin da na gaya miki ba, har yanzu ko shimfida ba mu hada da shi ba, ballantana ya kusance ni”.

“Na sani, ba za ki yi min karya ba”.

Ta shiga kokarin bude jaka. Wata ‘yar karamar kwalba ta dauko.

“Kin ga wannan a abincinsa za ki saka ko a shayi, na rantse miki komai taurin kansa sai ya rusuna, za ki ga yadda zai dinga yi miki magiya, ke kar ma ki je gurinsa, da kansa zai zo ya durkusa a gabanki yana rokon’.

Nabla ta saki hun murna.

“Ka aminiyata kin gama mn koma, dole ne na ba ki tukwici, wallahi ko zai ci kaniyarsa, sai na wajiga shi, ke sai ma ya siya, zai gane kurensa”.

“A’a ki dai bi shi a hankal, ban kawo miki don ki gara shi ba, kin ga idan ki ka y haka kin kor gaba”.

“Ke haba, ni na isa? Yadda nake son Yayana ba zan ya ba”.

Sai bayan sallar isha Kabir ya zo suka wuce.

Washegari da sassafe Deedat ya dira, Ummi ko ta shiga y masa fada ta inda ta shiga ba ta nan ta ke fta ba, a fadan nata ta fahimci Nabila ta sanar mata rashin hada shimfida da bai yi da ita ba. Kwakkwaran motsi kasawa ya yi, gaba daya ya ji ya kara tsanarta, ya sani shi kam bai y dacen mata ba.

Ya sassauta murya, “Ummita, ki yi hakuri ba zan sake ba, na tuba”.

Har ya bar gurin ba ta sakar masa fuska ba, dole ya mike cikin rashin kuzari, da yake akwai mukulli a hannunsa, budewa ya yi kawai.

Ko ina na gidan kaca-kaca, ga an cicci abinci an zuzzubar, kamar cin abincin kaji. Komawa ya yi sashin masu aiki, Dije ya kira. Ta durkusa a gabansa.

“Dije me ke faruwa ne na ga gida ko na kaca-kaca?”

“Ranka ya dade ba ta tashi da wuri ne, da na kan kwankwasa domin gyarawa, sai ta ce na dinga bari sa ta tashi, kuma ta kan kai har sha biyu ba ta bude ba”.

Ya jinjina kai, “Shi ke nan, je ki”.

Ya gama koma, kama wanka da kimtsa daknsa, ba ta da alamar farkawa ya koma ya zauna a sitroom zucyarsa sai faman tafasa ta ke, yanzu kenan haka rayuwarsa za ta c gaba da tafiya? Shn wannan wacce irin mata Allah ya hada sh da ita?

Lokacin da ya ji motsinta ya dubi agogon da ke manne a jkn bango, karfe goma sha daya saura kwata. Ya ja tsak, daida lokacin ta fito da alama kayan da ta wuni da sh ta kwana duk sun cukurkude. Tana hango shi cike da farin ciki ta nufo shi.

“Yaushe ka dawo? Sannu da hanya, ina kwana?”

“Ki fara gada Ubangijinki kafin ni, ina nufin ki yi sallah”.

Ta yatsina fuska, “Eh man na y mana”.

Kai da jn yadda ta amsa ba ta yi ba, ya daure fuska tam!

“na son yanzu ki sake”.

“Ban gane ba”.

“Sallar za ki yi”.

“Na ce da kai fa na yi”.

Ya ce, “Ni kuma na ce ki sake yi”.

Ta turo baki tana kunkuni, sati guda ba ya nan ya dawo ko kadan bai dokanta da ganinta ba, ita kam gaskya ta gaji.

“Me ki ke cewa?”

Ta ce, “Ba komai”.

Ta shige bathroom ta burbura alwalarta ta fito, da kansa ya dauko darduma ya shimfida mata, sannan ta hau ta yi sallar. Tana darwa ya sake dubanta.

“Yanzu me ya rage?” Ya tambaya cikin kafe ta da manyan idanunsa wadanda ke karya dukkan garkuwar jikinta.

“Sai abin da ka ce”.

“Good, wanka za ki yi”.

Ido waje ta dube shi.

“Haba Yaya ba ka ganin sanyin da ake yi? Ka bari mana sai anjima”.

“Bana son gardama”.

Babu yadda ta iya, haka ta mike ta shiga ta yi wankan.

“Yauwa ko ke fa?”

Mikewa ya yi, “Zan dan fita”.

Takaici bai sa ta ce da shi kala ba, tab! Ashe da ma kallon kitse ta ke ma rogo, babu abin da ya ya, ba soyayya, ba ya kalama masu kwantar da hankali, sam bai iya tafi da mace, ta sani ba rashin son ta ne ya mayar da shi haka ba, kawai ya kasa wayewa ne ya mai da kansa ustazu, ko ya ke Ummi ce ta ke dan kwafar masa da gwuiwa, ta ki bari ya walwala, Allah ya dora ta akan maganin Aisha, zai gane kurensa, dan hirar da ya ke zuwa gurin Ummin ma sai ta kansile shi.

Dije ta kira ta taya ta kintsa ko ina na gidan, da taimakon Dije suka yi girki, duk da wani abu da ta dafa sai da ta bishi da magnin Aisha, har cikin tea din da ta dafa, ta sani in yaso ya gwanya mata zai ce ya koshi amman ba zai fasa shan tea ba, dan haka tafi tsugawa a shayin. Bayan magriba ya dawo, abinci a jere a darning na rana ya tadda na dare, ta so nuna bacin rai, sai dai tasan hakan bazai dame shi ba, hasali ma zaifi farin ciki da hakan, haka ne ya sa ta bata ma tambaye shi dalilin rashin dawowar sa da rana ba, ya kamata a ce ta burge shi gurin shigar da ta yi, sai dai ko kadan ba ta burge shi ba.

Kananan kaya ne masu kama jiki, ita daban kayan daban, tumbinta ne ya lalata tsarin komai, kirar jikin ta komai na ta ba sa cikin tsarin matan da ya ke so ya aura, halaiyara ta, rawar kai, surutu, fadi ba a tam ba ye ka ba, shishshigi, gajeriya ce,  mazaunanta sun yi mata yawa, a kwaisu sai dai yana yin su sam ba sa birge shi, ba ta da man yan nono, a nanike su ke a jikin ta.

“My lobe sannu da dawowa,”

Sam hakan d ta fada bai yi armashi a bakin ta ba, ta zauna a kusa da shi kamar za ta shige cikin sa, gaba daya ya gama takura, ba ya son gwaleta.

“Nasan za ka bukaci abinci,”

“An ya kuwa”

Ta shagwabe murya.

“Nafa bata lokaci gurin shirya ma ka ban bar su Dije sun yi girkin ba, da kaina na girka ma ka,”

“Nabila na koshi naci an ji ma”

“Ok shi kenan, amman dai ka sha tea ko?”.

Ta shiga kici niyar bude flast ta tsiyayo a Cup,  yadda ta ke rawar jiki tausayinta ya jiduk kuwa da babu masaka tsinke a cikin sa haka ya kama sha, ta na ta jan sa da hira, lokaci lokaci tana fakan idon sa ta tintsire da dariyar mugunta, ya mike, ina son zan huta na gaji, gani ta yi yanufi Bed room din sa, ta sheke da dariya ta mike a doguwar kujera.

“Dan rainin hankali yau zanga karshen girman kai, ta yi kwafa”.

A can dakin sa an ta shi maza a tsaye, sai faman kai komo ya ke, yana jinsa cikin wani yana yi da bai taba jin sa ba, hankalin sa yayi matukar tashi da yaga yadda ya koma, kunyar kansa ya dinga ji, rigar da ya cire ya rage daga shi sai singlet da gajeran wando, komawa yayi ya maida ta kunyar kansa yake ji, ya ya zai yi?

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un ya shiga maimaitawa, in ya zauna sai ya mike ya koma bakin kofa yana leken Nabila.

Tana lura da shi, ta san hakan za ta faru, tuni ta dade da sanyo fitinannun kayan baccinta wanda ba su da maraba da abin tata, ta yi wata mika dukkan cinyoyinta suka bayyana.

Ya runtse idanu ya bude, ya koma ya zauna, kai ya ji ba zai iya ba, ya kai kololuwa bai san sa’adda ya nufi sitroom ba.

Ta yi saurin rufe ido tare da yin wata mika, tsayawa ya yi cak! Yana tunani, kada fa ya je gare ta ta raina shi, kuma dole in za a yi irin wannan sabgar sai an rage kayan jiki, ta ya zai bari ta ga jikinsa? Kai ba zai iya ba, gwara ya hakura ko da zai mutu. Ya ja tsaki, kokarin juyawa ya yi.

Ras! Gabanta ya buga, wai shi wannan wane irin mutum ne? Yana nufin ya gwammace ya azabtar da kansa? Da sauri ta mike zaune.

“My lobe lafiya na ganka haka?”

Ai ko ya daure fuska.

“Me ki ka gani?”

“Na ganka ne kamar…”

Ya kafe ta da ido yana tsoron kada dai a ce ta gane. Da sauri ya katse ta.

“Cikina ne ke ciwo, kina da kanwa?”

Kamar ta sa ihu, me zai hada shi da kanwa? Ta san makarin abin yake nema? Ba za ta bari hakan ta faru ba.

“Ni ban ma taba ganinta ba, sai sunanta kawai da nake ji ballantana na ajiye ta”.

Ya ja tsaki ya koma daki. Ta saki baki tana kallon ikon Allah. Karshe rufa masa baya ta yi.

Yana kwance a gado sai faman juye-juye yake, ya dago kai.

‘Me kuma ya kawo ki dakina. Kin mancde sharadina ne?”

Zuciyarta ta kara macewa da sha’awarsa, ba za ta iya jure rashinsa ba yau, ba za ta bari wannan damar ta wuce ta ba, ko da kokawa sai ta tabbatar ya ba ta hakkinta. Ba ta san sanda ta manne a jikinsa ba, hakan ya kara haddasa mata wani irin tsananin sha’awa da jin dadi a zuciyarta. Kamshin turarensa ya gama kashe mata jiki, ba ta san sanda ta shiga shafa ko’ina na jikinsa ba.

“Ina matukar sonka Yayana”. Ta fada.

Tuni Deedat ya mika wuya, abin da ta ke masa ya ji dadi, ta gama kashe masa jiki. Rungume ta ya yi sosai a jikinsa har sai da ta dan yi kara, wani irin shauki ta ke ji.

“I lobe you! I lobe you!!” Ta dinga maimaitawa.

A hankali ta ji yana lasar wuyanta, yana zira harshe cikin kunnenta, yana fidda numfashi daidai, yana sumbatar ko’ina na jikinta.

Rikicewa ta yi, ta fita hayyacinta, gaba daya suka fada wata duniya, musamman ma ga shi wanda bai taba tsintar kansa a irin wannan duniyar ba.

Daga bangaren Nabila kuwa, ta saba mu’amala da maza iri-iri, au kam ta tabbatar sauran maza suka rako, yau ta tabbata Deedat ya cika gwarzon namiji. Babu namijin da ya taba gamsar da ita irin haka. Ba ta taba dandanar irin wannan zumar ba, ba ta taba cin karo da wanda ya iya rikita mace har ta dinga kokarin shidewa kamar Deedat ba.

Ba za ta taba son ya yi nisa da ita ba, tabbas ta yi wa sauran mata zarra, Deedat daban yake a cikin maza, jarumin jarumai ne. shi din goga ne ta ko’ina, ba ta taba samun nutsu kamar yau ba, duk wani burinta da mafarkinta a kan Deedat ya gama cika, haukan son da ta ke masa kuwa sai ya karu.

A haka bacci ya yi awon gaba da su.

Kwalla kiran da aka yi a masallacin da ke jikin gidansu shi ya haddasa farkawarsa, ya bude ido. Yunkurawa ya yi zai mike ya ji Nabila kankame a jikinsa a cikin bargo. Da gudu ya janye ya diro a gado, sai ya lura babu kaya a jikinsa, ya rarumi jallabiyarsa ya zira.

Wani tashin hankali ya shiga, abubuwan da suka faru suka shiga dawo masa. hannu ya dora a ka, yana jin zuciyarsa kamar za ta yi bindiga, duk gwiwoyinsa sun gama sagewa ya shiga bathroom ya yi wanka irin wanda addini ya shar’anta, wato wanda ya kusanc matarsa, hade da na soso ya daura alwala. Cikin sanda ya shirya yana jin kunya, ba ya son ta farka, sum-sum ya yi waje.

<< Kyautar Zuciya 20Kyautar Zuciya 22 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×