Wayarsa ta dauki ruri, ya daga. Muryar Nurat a sanyaye.
“Mu yi addu’a, za mu samu mafita ka ji, ka ga Yayata tana sonka, a dalilinka ta canza, kowa na jin dadin canzawarta kada ka dauke mata farin ciki. Kai ne farin cikinta…”
“Ni kuma ke ce farin cikina, don haka ina son kaina”.
“Ina jin yadda ka ke ji… zan ajiye waya na ji Ammi tana kirana”.
“Zuciyata na yi min ciwo, na rasa da me zan sanyaya ta”.
“Ni ma ina jin haka na ce da kai, cutuka iri-iri ne, amma ba na tunanin akwai mai. . .