Ya ci gaba da sambatunsa kamar wani tababbe ko karamin yaro.
Idan ta tuno hirarsu da Aazeen duk sai dadi ya kamata, yanzu ta ina za ta fara? Ta yi shiru cikin tunani. Ta yi murmushi, me ya sa ta damu da yawa? Me ya sa zuciyarta ta nace da son hada dangantaka da Adamu?
Ta gyara zamanta, “Kila shi ne sanadin gyaruwarta, sai kun hadu zai gane wace ke na sani, ba zai guje ki ba a lokacin da ya san halayyarki, don haka nake son in kama zuciyarsa da zummar ke ce, kuma ai ni ma mace ce. . .