“Na kasa samun nutsuwa, farin cikin rayuwata na fushi da ni”.
Nurat ta dube ta don gaskata abin da kunnuwanta ke jiyo mata.
Aazeen ta dafe kuncin Nurat da hannu biyu ta dago fuskarta.
“Ko ba haka ba ne kanwar?”
Nurat ta yi murmushi, har kumatunta na lotsawa.
“Okey yanzu na amince da zabin abar kaunata, shi ke nan?”
Nurat ta buga tsalle.
“Yayata da gaske ki ke yi?”
“Eh ana”.
Ta rasa inda za ta tsoma ranta saboda tsananin farin ciki.
“Saura kawai na ganshi. Allah ya sa dai kanwata ta iya zabe”.
Cike da farin ciki, “Yayata, dole. . .