Zaune take cikin shiri zuwa aiki, lokaci zuwa lokaci takan daga kai zuwa agogon da ke manne da bango. Umar take jira, tun dazu Hassan ya ce zai zo ta ba shi key din mota ya karbo mishi sako, Sai dai har zuwa lokacin da ta gama shiryawa Umar din bai zo ba.
Kamar daga sama kuma ta ji sallamar Umar din, dalilin da ya sanyata daukar mayafinta laptop din ta, sai kuma karamar jaka, ta nufi babban falon.
Zaune ta iske shi ganinta ya sanya shi zamewa kasa hade da gaishe ta, har kunyar irin respect din da Umar. . .