“Dan Allah, kada ka ƙara kusanta tata, kada ka ƙara nema na, kada ƙara bin ko da hanyar da kasan za mu haɗu ce, wannan roƙona ne gareka…”
Kuma ta na kaiwa nan ta fice daga motar. Raja ya yi murmushi ya na ɗaga kafaɗarsa ta dama, wai kada ya ƙara nemanta, ai abun da ba ta sani ba shi ne; shi da ita kuwa yanzu suka fara haɗuwa, don ba zai rabu da ita haka ba, dole zai san yanda ya yi ya aureta. Sai da ya gama shawaginsa a duniyar tunani, kafin ya tayar da motar ya juya ya bar unguwar.
Da sallama a bakinta, Rabi ta shiga gidansu, duk da akwai duhun dare, ta na iya ganin komai dake wakana a tsakar gidan, saboda hasken wutar lantarkin dake ci a tsakar gidan.
Zaune a kan babbar tabarma Habiba ce, Fatima, da kuma Mahmud, sai Babansu daga can gefe ya na sauraren radio, daga Habiban har Ɗan Lamin miƙewa su ka yi suna kallonta.
A dai-dai lokacin Saratu dake zaune a ɗaki ta fito da gudu, jin wata murya me kama da ta Rabi, hasken ƙwan lantarki nan, ya haska mata fuskar Rabi tar, kusan sati huɗu kenan rabon da ta saka ‘yar uwar tata a idonta, kuma duk tsawon wannan lokacin ita kaɗai ce take cikin damuwa a gidan, daga Ɗan Lami har Habiba babu wanda ya damu.
Ta na iya ga wata kallar rama da Rabin ta yi, ga kuma wani rauni da take iya gani a gefen fuskar Rabin.
“Gantallaliya an dawo?”
Kalaman Habiba kenan, hakan ya sa da maɗaukakin mamaki Rabi ta kalleta, wato matar nan ba ta san Allah, ita take turata aikatau, kuma a hanyar dawowarta gida daga wurin aikatau ɗin aka saceta, har kusan sati huɗu ba ta gida, amma da abun da za ta fara tarbarta da shi kenan?.
“Gantali?, haka aka ce miki gantali na tafi?”
Ta tanbaya ƙwalla na ciko idonta.
“Yo in ba gantali kika tafi ba a gidan uwr wa kike tsawon wannan lokacin?!”
“Gidan uwr da kika aike ni na je, ko ba ki ji ba?, na ce gidan uwr da kika aike ni na je!”
A wannan lokacin kam Rabi ta je ƙarshe, ba za ta iya jure ko wani cin kashi ba, a yanda take jinta ba za ta iya ɗaukar ko wani ciwon kai ba, bayan wanda take tare da shi, haba!, abun ai ya yi yawa, ya kamata ace an barta haka, ko ita ma ta huta. Ba wulaƙancin Habiba kaɗai ba, na kowa ma ba za ta ƙara ɗauka ba.
Habiba ta shiga tafa hannuwa cikin sallallami.
“Rabi? Ni kike zagi? Ki ce dadiron naki rashin kunya ya koyar da ke?”
“Ni ba karuwa ba ce. Wannan gantallaliyar ‘yar taki da ta bar gidan ubnta ta bi namiji ita ce karuwa!. Ya isheki haka Habiba, na gaji, ba zan ƙara ɗaukan wani walaƙancinki ba, ya isheni haka!”
“Ɗan Lami ai ka na ji ko?, To ka koreta daga gidan nan, dan ba zan iya zama da ita ta na halin ‘ya’yan akuya ba. Ban da rashin kunyar da ta koyo kuma!”
Kamar da aka kunna inji haka Ɗan Lami ya hau zagin Rabi, ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba, Rabi kuwa ta na tsaye a gabansu ƙyam, babu wani alamar tsoro ko rauni tare da ita, to wani dare ne jemage bai gani ba?, ai na mutuwarsa ne kawai ya rage. Abu da ya yi ƙamari Ɗan Lami ya rarumo muciya ya yi kan Rabi da ita.
“Kar ka soma Abba!”
Ta dakatar da shi a dake, hakan ya sa Ɗan Lamin ya tsaya daga shirin dukanta da yake, doj da ma duk borin kunya yake, ya na yi ne dan ya burge Habiba, saboda akwai maganar kuɗi tsakaninsu.
“Kar ka soma duka na. Wani laifi ma na maka da na cancanci duka huh?, yau sati na uku ina kwance a asibiti, an samu wasu marasa imani sun haikemin, kuma ba komai ne ya ja min hakan ba face ayyukanka, ayyukanka marasa kyau da ka saba yi, zina da kake yi da ‘ya’yan mutane ita ce yau ta faɗo kaina, bayan ta faɗa kan ɗaya ‘yar taka, kai babu ruwanka da rayuwarmu, shagalinka kake san ranka…”
A take Ɗan Lami ya ji jikinsa ya yi sanyi, dan duk abin da ta faɗi gaskiya ne, babu abu ɗaya da ta faɗi wanda yake ba dai-dai ba, sai dai kuma waɗanan kuɗaɗen da yake hangowa ba za su su sa ya ji maganar tata ba.
“Ki fice ki bar min gidana, kada ki sake dawowa gidan nan!”
Zuciya ta ciyo Rabi, hakan ya sa ta juya ta fice daga gidan, da gudu Saratu ta bi bayanta tana kiranta, ko hijabi babu a jikinta haka ta fita.
Habiba ta samu wuri ta zauna, kamar ta tashi sama dan murna, dan kuwa duk abun da take so ya tabbata, rayuwar Rabi ta lalace, tun da har ta furta da bakinta cewar wasu sun mata fyaɗe, sai a yanzu ne burinta ya cika, sai a yanzu ne duk fafutukar da ta yi ta yi tun bayan auren Maryam ta kawo ƙarshe.
“Wallahi sai na ga bayanki ke da yaranki, ba zan huta ba sai na ɗai-ɗaita rayuwarki Maryam!”
Haka ta taɓa faɗawa Maryam ɗin, a wani lokaci can baya, kuma ga shi ta yi ɗin, ta aikata duk abun da ta ci buri, ita ce fa Habiba, babu wani wanda ya isa ya shiga.
*****
Let your wings be soft enough to carry her, until she remembers how to fly again…
RABI’A POV.
“Rabi!… Rabi!”
Kiran da Anti Saratu ke mata ne ya sa ta tsaya da tafiyar da take a fusace, ta juya tana kallon Anti Saratun, wadda fuskarta ta yi gaje-gaje da hawaye.
“Rabi”
Ta furta a raunane ta na rungume Rabin, tare da fashewa da kuka, har mutanen dake wucewa ta lungun suna kallon su, duk dauriyar Rabin sai da ta zubar da hawaye, Anti Saratu ta saketa ta na dudduba fuskarta ta ɗan hasken dake layin.
“Rabi ina kika shiga haka?… Kusan kullum sai Fu’ad ya je nemanki makarantar da kike aiki, amma haka zai dawo yace min ba a sameki ba, har police station ya kai ƙara, amma babu wani bayani”
Rabi ta ɗan yi murmushi ta na share hawayenta, a ƙalla de tana da wani wanda ya damu da ita a duniya, Allah ya sa har yanzu akwai wani wanda yake santa har zuciyarsa, kuma ta san da ma duk wannan tsawon kwanakin da ta shafe bata gidan babu wanda zai nemeta bayan Saratun.
“Ƙaddara ce ta zaunar da ni a can, ƙaddarar da Allah ya hukunta faruwarta a kaina, irin abun da mahaifinmu yake shi ne aka aikata min, mutum biyar Anti Saratu, su biyar suka haikemin!”
Saratu ta ƙara fashewa da kuka ta na rufe bakinta, tare da girgiza kanta.
“Ki dena kuka Anti Saratu, ya wuce fa, Allah ya hukunta cewar dole sau hakannta faru da ni, kuma ga shi ya farun!”
“Yanzu ina za ki je?”
“Gidan kawu Habu zan tafi”
Ta faɗa don ta san babu inda za ta iya zuwa a yanzu da ya wuce can ɗin. Anti Saratu ta gyaɗa kanta tana saka hannu a aljihun doguwar rigar jikinta, sannan ta zaro kuɗi wurin dubu goma ta kamo hannun Rabin ta danƙa mata.
“Ga shi, ban sani ba ko za su amfane ki”
Rabi ta karɓa, sannan ta gode mata, Saratu na tsaye a ƙofar gidan har Rabin ta fice daga lungun.
Rabi na fita daga lungunsu ta wuce shagon Yaya, don ba za ta iya zuwa ko ina ba tare da ta sanar masa da halin da take ciki ba.
“Ka yi shiru Yaya?”
Rabi ta faɗi cikin hawaye, yayin da take zaune a kan benci tana kallon Yaya, bayan da ta gama tsara masa duk halin da ta shiga, da farko da Yayan ya ganta ya yi farin ciki, amma tun da ta fara bashi labarin abun da ya faru da ita sai ta ga yanayin fuskar Yayan ya sauya.
“Ba komai”
Yayan ya faɗi ya na kawar da kansa, mamaki ya bala’in kama Rabi, yau ita Yaya yakewa magana a haka?, ita ce ta masa magana ya amsa mata ciki-ciki?, me yake faruwa ne?.
“Yanzu ya kake ganin za ayi”
“Ai yanda za ayi kawai shi ne ki kama gabanki, dan ni babanmu ya min mata, kuma nan da wata ɗaya za ayi auren!”
Da farko sai da Rabi ta ji wani irin duka a ƙirjinta, daga baya kuma sai ta yi murmushi me ciwo, to ita wai yanzu ma miye zai bata tsoro ne?, ai taskun rayuwa ba yau ta fara shigarsa ba, halayen ɗan adam babu kalar wanda bata gani ba, uban da ya haifeta ma ya ƙita, waye wani Yaya?, da dan har ya gujeta za ta ji ciwo?, ai da ma haka rayuwar take, wani zai soka da yini, sai ya ƙika da daddare,wani da ma can ba da zuciya ɗaya yake sanka ba, amma kai da ka so shi da zuciya ɗaya idan ka yi haƙuri Allah zai nuna maka ƙarshensa, ga shi yau ita ma ta ga zahirin Yaya.
Hawayenta ta goge, dan babu amfanin barinsu su zuba, ba za ta ƙara barin hawayenta su zuba a gaban wani ba, ko kukan za ta yi gwara ta ɓoye a wani wurin ta yi, ganin hawayen mutum na ɗaya daga cikin lagonsa, ‘A strong woman will always turn pain into power’ haka ta faɗawa kanta, dan haka za ta yi iya bakin iyawarta don ta yaƙi abun da zai durƙusar da ita, saboda haka Yaya bai bata mamaki ba.
Miƙewa ta yi tana murmushi ta kalli Yaya a tsakar ido tace.
“To Yaya, Allah ya sanya da alkairi, ka gaida sabuwar amaryar, ni na tafi, sai bayan saduwa kuma!”
Daga haka ta juya ta fice. Yaya ya ja wani dogon tsaki ya na jan wayarsa, shi mahaukacin ina ne zai yarda ya aureta bayan ta faɗa masa cswar maza har biyar sun mata fyaɗe?, ai yanzu a yanda take bata da maraba da karuwa, ko karan hauka ne ya cije shi ai ba ya yi wannan gangancin ba, gwara ta je ta can, ta ƙarata, wata ƙila ta samu wani ɗan tasha kamar babanta, sai ya temaka mata ya aureta, amma shi dai bai ga abun da zai yi da ita ba, da ma ba ita kaɗai ba ce budurwarsa, idan auren yake so ai sai ya zaɓi ɗaya daga cikin ‘yan matansa ya ce zai aura, amma ba Rabi ba, dan a yanzu ta riga ta zama tarihi a rayuwarsa, shi da ma can don kyanta yake santa, yanzu kuwa da aka mata bajo a fuska ubn wa ya aikeshi aurenta.
“Haka shi Ɗan Lamin yace”
Cewar kawu Habu, bayan da Rabin ta gama masa bayanin abun da ke faruwa. Dan tana barin shagon Yaya gidansa ta nufa, durƙushe take a gabansa, yayin da shi kuma yake zaune a kan kujera. Rabi ta gyaɗa masa kai, idanunwata a bushe ƙamas, babu wani damshin ƙwalla ko ɗaya a ciki.
Kawu Habu ya ci gaba da kallon Rabi cike da tausayi, ya girgiza kansa sannan yace.
“Babu damuwa, tashi ki shiga ɗakin Laure”
Miƙewa ta yi sannan ta shiga ɗakin matarsa ta biyu, wato Anti Laure, mace me kirki da karamci. Yaranta biyu da Kawu Habun.
Zama ta yi daga bakin gadon Anti Lauren, inda ta sameta tana matsar ƙwalla, kasancewar inda suka yi maganar kusa da windown ɗakinta ne, dan haka Rabi ta fahimci cewar zancen nasu ta ji.
“Sannu kin ji Rabi”
Rabi ta yi murmushi ta na kauda kai.
A hankali Ramatu matar Kawu Habu ta farko ta saki labulen ɗakinta, bayan da ta gama leƙen kawu Habun da Rabi, sannan duk abun da suka tattauna kaf a kunnenta, ita kuma a matsayinta na aminiyar Habiba, ba za ta yi shiri ba tare da ta sanar mata da labarin ba.
Dan haka ta lalubo wayarta ta fesawa Habiba kaf abun da ya faru.
Cike da takaici Habiba ta wurga wayarta kan gado, bayan da ta gama sauraron bayanan Ramatun, ita ta ma manta da gidan Habun, ta manta cewar idan aka kori Rabi daga nan can za ta nufa, amma ba komai, wannan ma ba zai gagara ba, ita ta san abun yi.
No.181,Guzape, Abuja…
MISHAL POV.
Tana kunna tv a falo aka turo ƙofar falon, hakan ya sa ta juya da sauri ba tare da ta kunna tvn ba, yanayinsa kawai ya bayyanar mata da halin da yake ciki, don ta riga da ta gama gane shi, abu ƙanƙani yake fusata zuciyarsa, kuma kusan kullum haka yake dawowa gidan.
Ba ta ce masa ƙala ba face kallonsa da ta yi har ya wuce ɗakinsa, dan ta riga ta gano cewar idan ya na a fusace baya san a masa magana. Bakinta ta taɓe ta kunna tvn, sannan ta juya ta koma kitchen.
Girkinta ta ƙarasa, sannan ta ɗebe komai ta shirya a kan danning. Ta dawo falo ta zauna tana kallo, ba ta shirya masa magana ba sai bayan shuɗewar muntuna kusan ashirin. Ta miƙe daga kan kijera, sannan ta nufi ɗakinsa.
Bata ƙwanƙwasa ba, dan ta san ko ta ƙwanƙwasa ba lalle ya amsa mata ba, yaya lafiyar kura, balle ta yi zawo, tsaye ta ganshi jikin mirror, ya na taje sumar kansa. Ta ci kin mirror kawai ya kalleta, sanye take da wata farar off shoulder shirt, sai wani baƙin short culottes, wanda bai ƙarasa kan guwarta ba, ya ɗauke kansa ya na ci gaba da taje sumar kansa.
Mishal ba ta damu ba, dan idan da sabo ta saba da wannan abun nasa , babu me iya zama da Kuliya sai me haƙuri, tsayawa ta yi a gefensa tana kallonsa, amma bai ko kalleta ba, sai ta rakaɓa ta gefensa ta shiga gabansa ta tsaya, wata gajeriyar harara ya maka mata, sannan ya kauce ya na ci gaba da tazar, Mishal ta ƙara matsawa ta tsaya a gabansa, sannan ta saka hannayenta ta karɓi matajin hannunsa, ta yi tattage dan ta ƙara tsayi, sannan ta shiga taje masa sumar.
Memakon ya tanka mata, sai ya mata banza ya juya ya barta tsaye da matajin a hannu, Mishal ta girgiza kanta ta na mitar halin wanga bawan Allah, sannan ta aje matajin a kan mirror, ta biyo bayansa.
Zama ya yi a bakin gado ya na kawar da kai. Mishal ta yi murmushi ta na tsayawa a gabansa, hannunta ta sa ta kamo haɓarsa ta juyo da fuskarsa gareta.
“Me nene?”
Fuskarsa ya ƙwace sannan ƙara juyar mata da kai, sunkuyawa ta yi ta kai hannunta kan buttons ɗin gaban rigarsa ta buɗe guda huɗu, duk bai kulata ba, sannan ta hau kan gadon ta zagaya ta bayansa, ta tsaya a kan gwiwoyinta, tare da saka hannayenta a kan kafaɗunsa, ta fara masa tausa.
“Me nene ?”
Muryarta ta tambaya bayan wani lokaci, memakon ya amsa mata, sai ya saka hannunsa na dama ya kamo nata, tare da ƙoƙarin janyota zuwa gabansa, hakan ya sa ta miƙe ta sauƙa daga kan gadon ta tsaya a gaban nasa, sai kuma ya kamo hannunta ya zaunar da ita a kan cinyarsa ta dama.
Ya ɗaga kafaɗarsa ta dama ya na sofara gashin da ya sauƙo mata kan fuskarta a bayan kunnenta, a lokaci guda yana kallon fuskarta. Mishal ta lumshe idonta ta buɗe, sannan a hankali hannayenta suka kewaya bayansa, kafin ta saka kanta a cikin wuyansa.
“Me ya faru ?”
Muryarta ta fito a kan fatar wuyansa, yanayin ya sa Kuliya lumshe idonsa sannan ya buɗe, ya saka hannayensa ya ƙara rungumeta a jikinsa.
“Game da binciken yayarki ne…”
Sai kuma ya yi shiru. Mishal ta sumbaci wuyansa ta na ƙara matse hannunta a bayansa.
“Ummhum?”
Muryar tata ta kuma faɗi a wuyansa.
“Me gadin makarantar ku ne yake san ɓatamin rai, yau da na je, babu yanda ban yi da shi ba kan ya ba ni wasu bayanai, amma yace wai sai na nemo izini daga sama, shi ne na…”
Jin ya yi shiru ya sa Mishal ɗan ɗagowa daga jikinsa ta kalli fuskarsa.
“Ka mare shi, right?”
Sai shi ma ya sunkuyar da kansa ya na kallonta.
“Rai na ne ya ɓaci”
“Na fahimta, amma ba haka ake ba, kamata ya yi ace ka tafi da yaranka, sai ku je a matsayin jami’ai, waɗanda suka je bincike, ko principal ba zai baku matsala ba”
Kuliya ya rage girman idonsa ya na kallonta, me ya sa shi be yi tunanin hakan ba?, ya sumbaci goshinta ya na ƙara janta jikinsa.
“I love you Teddy Bear…”
Mishal ta yi murmushi.
“I hate you Abu Aswad….. Na gama abinci, mu je ka ci”
Ya gyaɗa mata kai ya na ɗagata daga jikinsa.