Ya tafi da sauri da niyyar zubewa a ƙasa gabanta ta dakatar da shi ta hanyar ɗaga masa hannu.
"Zauna kan kujera, kar ka zauna a ƙasa." Ta faɗa a dake, kamar bata fahimci abinda yake niyyar yi ba.Jikinsa a sanyaye ya nemi guri kan kujera ya zauna, zuciyarsa cunkushe da tunani da saƙe-saƙe. Iyayensa sun tabbatar masa Ummanmu ta yafe masa, amma daga irin kallon da take masa na yanzu babu abinda ya canza daga na baya. Kallo mai bayyana tsana ƙarara, mai ɗauke da saƙon jin haushi da tarayya dashi a dolen. . .