"Wannan shi ne yaron da kika ce kina masifar so?"
Alhaji Abdurrashid ya tambayeta yana sake ƙure hoton Khamis da kallo, hoton da ya mamaye gaba ɗaya fuskar wayar Rufaida.
Shagwaɓe fuska tayi kamar za ta fashe da kuka, ta ƙara tura baki gaba, kamar baza tayi magana ba, sai kuma ta buɗe baki a shagwaɓe ta ce"Daddy dan Allah..."
"Saurara Mamana."
Ya katse ta cikin tsawa-tsawa da muryarsa a fusace, wani abu da shi kanshi bazai tuna lokaci na ƙarshe da yayi mata ba.
Lumshe idanu yayi, yaja nannauyan numfashi ya sauke, ya nemi. . .