A fusace ta miƙe tsaye daga zaunen da take tana cewa,
"Ƙarya kike yi wallahi kawata! Sai dai in baza ki faɗa min ba. Amma taya za'ayi haka kawai rana ɗaya kiyi irin wannan magagan arzikin bayan ba ruwan kuɗi ake yi daga sama ba? Sannan kuma ba tsintarsu ake yi a ƙasa ba?
Amma tunda haka kika ce, na kula akwai zamba cikin aminci a tsakaninmu. Talaucin da yayi min rumfa yasa kin fara guduna, kina so ki nuna min yanzu kin daina yi da ni. Ba komai, ni ce har zan nemi wani abu. . .