"Kuma..."
Bata san sadda ta ɗaga ɗan yatsarta manuniya ta ɗora akan laɓɓansa ba. Ta riga ta fahimci matsanancin son da yake yi ma yarinyar tun daga labarin farkon haɗuwarsu da ya bata. Don haka a yanzu babu amfanin yayi ta jaddada mata irin son da yake mata, wanda hakan ba ƙaramin luguden daka yake saka ƙirjinta yi ba.
'So tsuntsu ne. Yana tashi daga wannan bishiyar zuwa wancan.'A yanzu ne ta ƙara yarda da gaskiyar azancin maganar nan ta Malam bahaushe.
Katse shi da tayi ta hanyar ɗora yatsarta a laɓɓansa yasa shi dakatawa daga. . .
Innalillahi wa inna ilaihi rajiun Khamis ya shiga uku wallahi!