Akan idanunta Fadila ta taɓe baki, sai kuma ta ce,
"Oho! Wallahi rabona da shi tun jiya da safe da ya kawo ni makaranta."
Duk da yadda hankalinta ya ƙara ɗugunzuma sai tayi ƙoƙarin dannewa
"Ke da Yayanki Fadila? kuma babu ta yadda za ayi a san halin da yake ciki? Kin san bai da lafiya fa... kuma nayi ta kiran layinsa wayar ba ta shiga. Ya jikin nashi? Ya ji sauƙi?"
"Toh! Ya ji sauƙin kenan. Tunda lafiya ai ita ke ɓuya."
Fadila ta amsa da rashin damuwa. Mannirah ta buɗe baki za ta. . .
Ikon Allah
Me ke Fatima haka kuma? Kar wani abin ya sami Mannira dai