Dama kin yi hankali kin yi karatun ta natsu ki gane bata kanki da bakin kishin gidanku ya kamata kiyi ba ta wadannan yaran ya kamata kiyi ki tsaya kiyi musu tarbiya ki tsaya musu da addu’a, Ubangiji ya raya miki su ya kuma basu mazan da za su rike su.
Shima wannan yaron Mallam yana nan yana jiran shi don Alhaji Yahaya yaje yaga yawa Mallam irin bakaken maganganun da ya rinka gasawa mijinki sakaryar yarinya kawai shashasha mara wayo.
In sake jin kin kai wata magana can gidanku za ki gamu da ni, in kina da matsala. . .