Salatin shi na jiwo da karfi tare da jan tsaki mai tsananin karfi, kafin ya soma fadin “Kai wannan fitina da yawa take, ni Surajo naga abin da ya ishe ni, kin gani Fatima, tun dai ni a wurinki na gajiya ba kya ganin kokarina bare alherina komai nawa a raine yake a wurinki, bani da fita a wurinki ba ni da shi a gun danginki kiin zo kin same ni cikin iyalina kin takura mana kin tasa mu a gaba da dokoki komai aka yi ki ce baki yarda ba kin watsa min hadin kan gida kin raba. . .