Ina cikin haka naji kamar an yi min magana, a firgice na ce iye, na’am? A hankali ya bude baki ya ce min yi maza ki kulle kofa kar Mama ta shigo ta same ki, da gudu naje na kulle kofar na dawo na durkusa a gaban Ado, kuka sosai nake yi yayin da shi kuma yake kwance bai motsa ba lokacin ne na gane tsoratar da nayi ne ya hanani gane ya farfado, tun sanda na ji atishawa da hamdala sai nayi zaton ko daga wani wuri ne.
Muna cikin haka na ji isowar Mama tana fadin “Lallai. . .