Skip to content
Part 3 of 52 in the Series Mijin Ta Ce by Hafsat C. Sodangi

Ban san yadda aka yi ba sai kawai naga Hajiya Kubra tayi jifa da gyalen da take yafe dashi kan kace meye wannan tuni danbe mai tsanani ya kaure a tsakaninta da Mama, sai ji kake yi didim-didim-dididim!!

Don kuwa su dukkan su ma’abota kiba ne da kuma jin karfi, sai dai kan ka ce meye wannan Hajiya Kubra ta kai Mama kasa tim! Abinda ya firgita gidan gabadaya ni da kaina jikina rawa yake yi.

Habiba da ta kasa hakurin kayen da aka yi wa uwarsu, ta sunkuto tabarya da gudu tazo zata rafkawa Hajiya Kubra, cikin kuskure da rashin dace sai kawai ta sake timawa Mama tabaryar a gefen fuskarta da iyakacin karfinta, daga ita har Mama lokaci daya suka kurma wani irin ihu mai tsananin firgitarwa.

Habiba tayi waje a kidime tana neman taimako. Hajiya Kubra tana jin za su shigo tayi maza ta daga Mama dake kwance jina-jina ta sulale tayi ficearta, ta bar Mama tana yiwa makwabta rantsuwar Alkali ne kawai zai shiga tsakaninsu, su kuwa suna fadin “Abin dai kam bai yi dadi ba, a gefe kuma sai dariyar Mama suke yi don babu wanda bai san abin da gidanmu yake ciki ba.

Jinya sosai Mama tayi har da su zuwa asibiti, da su daukan hoto duk rantse-rantsen da ta yi tayi na daukan mataki  da kai magana kotu duk ya tashi a banza, iyaka dai ta sake tasa Babana a gaba da fitina wai shi din ya gajiya an shigo har cikin gidanshi anci mutuncin iyalinshi bai yi komai ba.

Kan haka har ta kira iyayenta suka zo suka sanya Babana a gaba ina jin shi yana mayar musu da bayanin yanda aka yi duka, su din ma dai basu gamsu da shirun da Baban yayi ba, sun ce in yana haka a gidanshi ai sai ayi abinda babu kyau, duk da dai sun gaya wa Mama rashin kyautawarta kan cin mutuncin abokin mijinta da tayi a gaban mijin nata.

Tun daga rannan kuwa ban sake ganin Mama tana yunkurin dukan Inna ba, don Hajiya Kubra ta gaya mata in ta yi miki laifi ki fada, amma duka tsakaninki da ita babu in kuwa ki ka yi ganganci ki ka yi, to nima zan yi miki irin wanda na iya, don ba baiwarki ba ce matar mijinki ce irin amfanin da kike yi mishi irinshi itama take yi mishi.

Ba kuma sai na ce miki yana sonta ba, tunda kina ganinta da ciki kina ganinta da goyo, don haka kin yi kadan fitinarki ta rabata da mijinta.” Wadannan bakaken maganganu na Hajiya Kubra sun sosawa Mama rai, don na ji ta tana nanata su a gaban Babana yafi sau nawa.

“Ni ina Humaira taje ne?” maganar da na sake jiwowa kenan daga cikin gidanmu, wacce tayi dalilin katse min tunanina, na dawo kan abinda nake ciki a lokacin bakin ciki da takaicin Mama suka sake lullube ni, don kuwa kowa ya sani zan yi mu’amalla da Mama ne kawai bisa tsoro, amma ba don so da kauna ba.

Wannan dalilin  ne ma ya sanya ni na zamo mai iya kwaikwayon Mama da al’amuranta duka babu wani abin da yake yin shi dabi’ar ta ne wanda bana kwaikwayon shi.

Ko a yanzu ma kuwa tsayawa nayi na shiga kwaikwayon maganar tata.

“Humaira.” Na’am, zo ga wanki, to na yi, Humaira, na’am zo ga shara, to nayi, Humaira, na’am zo ga aika, to na yi. Humaira, na’am zo…”

“Mama ki ke kwaikwayo?” da iyakacin karfinta tayi min tambayar, nayi maza na bar abinda nake yin cikin kaduwa na zuba mata ido ina kallonta, tsoro ya bayyana a fuskata. Habiba ce yata da nake bi ta dakin Mama, wata ashirin ne tsakanina da ita, abinda kullum Mama take nanata  gaya min kenan.

A duk lokacin da wani abu ya shiga tsakanin mu zata jaddada min ko sanda uwarki tazo gidan nan ta samu Habiba ne watanta goma sha daya, ke kuwa wata tara daidai tayi ta haife ki, don kamar a hannunta ta shigo dake. Bisa wannan bayani da Mama take yi minne ya zama dole in yi wa Habiba ladabi da biyayya, irin wanda bata yi wa uwata daya bisa gomanshi, tunda zata aike ni ta sani aiki ta yi min hukunci, ita kuwa tawa uwar bata isa tayi mata ba.

Sannan biyayyar da nake yi matan ban sa an sata tayi min adalci ba, wuni take yi tana jibgata da duka, ko da kuwa daga zaman cin abinci ne ko a wurin wasa, saboda Habiba na hakura da duk wani abin da ya shafi wasa, saboda yanzun nan zata rufe ni da duka, ko da kuwa ba da ita nake wasan ba, saboda rashin ‘yanci irin wanda nake ciki.

Ni har Suwaiba kanwar Habiba dake dakin Mama wacce ita din na girme ta da watanni tara dukana take yi, ban kuma isa in ce zan rama ba, sai Mama da Habiba su rufan min suce wai cin zalinta zan yi.

“Mama ki ke kwaikwayo, za ki gama da gamonki kema kin san saura.” Tayi maganar cikin yanayin jinjina kai alamar wai zan ji jiki kenan.

Na zobara baki na bata rai sosai, abinda nayi ya bata haushi har ta kawo hannu da nufin buge min bakin nawa, nayi maza na kabe hannun nata tare da fadin.

“A’a me nayi miki? Ban yafe ba.” Tayi maza ta sake kawo min wani bugun, nima na sake cewa “Ban yafe ba, muguwa kawai azzaluma.”

Ado ya leko cikin zauren, “Kai kuzo nan Mama tana kiran ku.” Ado shi ne yaron da Mama ta dauko daga kauyensu ta kawo shi gidanmu ta ajiye, ita da Babana suka hadu suka maida shi dan gatan gidan, saboda irin son da Maman take yi mishi.

Kanin ta ne uwarsu daya uba kuwa kowa da nashi, a wancan lokacin da ta kawo shi, shi din ba kowa ba ne face wani dan dogon yaro dan siriri dan baki, dan bagidaje-bagidaje, kana ganin shi kasan daga kauye yake, ko gajiya da aiki bai yi, don ya saba yin wanda ya fishi.

In kuma aka cika mishi kwano da abinci ya cinye shi tas, amma sannu a hankali sai aka wayi gari Ado ya murje  ya zama kosasshe ya zama wankan tarwada, ya zama dan gaye, ba zaka taba ganinshi ka gane bai dade da fitowa daga kauyensu ba.

Kan kace meye wannan? Sai gashi ya zama santalelen saurayi saboda ya samu ya dare kan dukiyar Babana, ba wannan ne abin da yafi komai kona min rai ba, irin zuwa gidan mu da ya yi da takardarshi ta kammala karatun Secondary wacce ko credit din da ake nema bai gama samu ba, amma ya gyara jarrabawar a gidanmu ya tafi (Federal Poly) yayi diploma ya sake dawowa ya shiga (A.T.B.U) yayi karatun digiri din shi.

Amma gabadaya nawa ‘yan uwan maza wadanda dukansu Maman ce ta haife su suna zaune a gida suna sakarci, sun ki karatu sun kuma ki tsayawa kan al’amuran Babana, su taimake shi kan harkokin kasuwancinshi sai Ado ne dai akan komai, amma wai Mama tana kallo hankalinta kuma a kwance bata da wata matsala.

Komai na gidanmu Ado ne yayi matukar shiga ran Babana, bai gajiya da yabonshi, yanzu zaka ji shi yana cewa “Jarumin yaro ne mai tsayuwa kan al’amuranshi gashi kuma komai kasa shi zai yi maka.”

Mutanen da suka san gidanmu suka kuma san Mama da dan uwan nata sun san Mama da Ado sune babbar matsalar da Babana yake fuskan ta amma ba rashin kasuwa ba.

Sai dai ita Mama kullum takan danganta matsalar kasuwar Baban nawa da yawan aure-auren da take cewa yayi, musamman wai auren shi na baya-baya wanda aka rufe mishi ido yayi ta kwasar dukiyarshi yana bayarwa.

Tun farko zuwan Ado gidanmu ba wani jituwa nake yi da shi ba, saboda bai taba shiga harkar Innata ba, bai taba samun lokacin daga ido ya kalle ta ba balle ya samu na lokacin gaisheta, haka nan ‘ya’yanta bai mu’malla da su iyakar shi Mama da ‘ya’yanta.

Don haka nima sai na zamo bana kallon shi, bana shiga harkokin shi, bana gaishe shi, bana sauraron shi don nima bana son shi.

Itama Mama mai ‘yan uwa ce da yawa, sai dai duk jama’ar da suka santa sun san bata wata mu’amalla ta ku zo ku gani da kowa sai da ‘yan uwan da ta hada uwa da su, bata damu ba ko uwa daya uba daya ko uwa kawai in dai uwa tana ciki to shi kenan.

Bisa wannan ne ma ta zamo ‘yan uwanta na wurin uba ba kasafai suke zuwa mata ba, saboda komai nisan garuruwansu da suka baro bata yarda bakuntar su ta wuce ta kwana uku sai ka ji tana yada magana tana fadin da aka ga ka zama mutun ne fa ake nemanka, amma kana karami menene ba ka gani ba?”

“Kwaikwayonki take yi Mama.”

Muna shiga ciki abinda Habiba ta fara fadi kenan.

“Kwaikwayo kamar yaya?” tayi tambaya don bukatar karin bayani, Habiba ta samu damar da ta tsaya rattaba bayani sosai da sosai na abinda ta tarar ina yi.

“Maman take yi wa wannan iya shegen?” Babana ne ya kara yin wannan tambayar, na dan kalle shi kadan can cikin zuciyata na ce tanfar dai yau ba a wurin Innata yake ba, kullum nan ne wurin zamanshi ko da kuwa girkin na wanene amma ita Innata ko girkinta ne, to sai ya faki ido yake shiga wurinta in dai ba kararta aka kai mishi ba zai je yayi mata hukunci nan ne zaka ga ya shiga kai tsaye.

Babu ruwan shi da wa ke da hakki saboda Mama bata yardar mishi baiwa mai hakki hakkin shi ba.

Abubuwan da Habiba ta kwatanta da suka bayyanawa Babana cewar maganar Mama da tafiyarta na tsaya ina kwaikwaya, ya baiwa Babana takaici mai yawa, zuba min ido yayi yana kallona, cikin takaici da bakin rai mai yawa, irin kallon da naga ya yi min din ya sanya ni nima na waiwaya baya don ganin wadanda suke tsaye.

Ado ne da Habiba wadanda su dukan su biyun ana cewa za’a kama ni za su yi sanadin da za a yi hakan.

“To ba dole tayi ta kwaikwayona ba, Habiba ai samu tayi duk abinda take yi ai ta sani gata gareta mai yawa a gidan, ga ta kuma ‘yar lelen Baba.” Ta karasa maganar cikin wani yanayi da ita kadai tasan abin da take nufi da hakan.

Babana  ya ce, “Ba fa na son kina yi min irin wannan maganar a gaban yara, ni na ce miki ina da wata ‘yar lele?” Mama ta ce, “Uhun, Alhaji kenan, bari dai in ja bakina kawai in yi shiru tunda ba ni da ikon yin magana, sai ka hayayyako min a gaban yara tunda ni ce marainiyar yaronka.

Amma in ban da haka iya shegen da wannan yarinyar nan take yi a gidan nan in da wani ne wanda ba a tsoron uwarshi da danginsu ai da bai kwashe kalau ba. Sai dai nima ba ina ganin laifinka ba ne kan hakan da kake yi, da azo ana tuhumarmu kan abin da bai taka kara ya karya ba, ai gara muyi ta hakuri da ita.”

Da irin wadannan kalaman kullum Mama ke tunzura Babana tasa shi yayi abinda take so, yayi min hukunci irin na azabtarwa, saboda babu abinda ta tsana a rayuwarta irin ta ganni ina zaune lafiya ko da kuwa ba wani walawa nake yi ba.

Shi kuma Babana ya kasa tunawa kanshi cewar su dangin Inna basu taba zuwa sun same shi kan wani abin da shi ko Mama ko wani can daban ya yi min ba, duk kuwa da sun saba ganina da tabon duka iri-iri a jikina, su kullum maganarsu kan tsaya ne kan abin da ya shafi ‘yarsu.

Sai ya yi ta biyewa Mama yana gana min azaba, ko da yake dai nakan gwammace nashi hukuncin komai tsananin shi akan na Mama, tunda ita bayan duka shake ni take yi ta tattara ni wuri daya ta hau kaina ta zauna, wai sai na ji nauyinta, ita din kuma ba karamin nauyi ke gare ta ba, don kuwa jibgegiyar gaske ce.

Mikewan da naga Babana yayi, ya sanya ni juyawa da gudu da iyakacin karfina, don nayi zaton kama ni zai yi, wajen juyawan nawa na banke Habiba dake bayana, shi kuwa Ado na kwantara mishi kwanon dake rike a hannuna, man gyadan dake ciki kuma ya kware mishi a fuska da jiki gaba daya.

Mama ta kama salati tana fadin, “Wai ga wani abin al’ajabi, wai ga abin mamaki ni majadan naga abinda ya ishe ni yake kuma nema yafi karfina.”

“Kamo min ita Ado, kamo ta maza in baka bulala ka hukuntata, ja’ira kawai mara kunya.” Babana ne mai wannan maganar, yayin da ita kuma Mama take fadin.

“Wannan shi ne wani zance kai baka hukunta al’amarin gidanka ba sai Ado? Kaja mishi kawai karin bakin jini itama ba so suke su bude ido su gan shi ba a cikin gidan nan.”

Babana ya biyo ni tsakar gida inda nake tsaye ina ta faman bari, ina kuma kuka saboda na riga na tsorata da abinda zai same ni. Innata kuwa tana sunkuye tana wankin kayan ‘ya’yanta bata daga ido ta kalle ni ba, balle ta ce “Me ke faruwa? Amma sai Babana ya shiga cewa shakiyancin banza shakiyancin wofi, mu nan gidan ba a kawo mana shakiyanci dama kin yi maza kin bari don masu koya miki ba riba zasu ci ba, wahala kawai zasu yi ta ja miki.”

Yana gama fadin hakan ya shiga shirba min bulalar dake rike a hannunshi, wacce yasa Suwaiba ta miko mishi, na shiga ihu ina buga tsalle ina faduwa a kasa don tsananin gigicewa.

Sai da Mama ta tabbatar na jigata ne ta fito daga falonta tana fadin “Ni fa bana son irin wannan ja min maganar da ka ke yi, kai kasan halin ja’irar yarinyar nan sarai ba a taba ta ba ma ihu take yi don dai ta kulla wa mutane sharri a unguwa ace to ga ta can ana azabtar da ita, tunda tasan muna tsakanin ‘yan sa ido to balle kuma an taba ta.”

Yana huci yake fadin “To ina ruwana da maganarsu, za su hana ni yin hukunci a gidana ne?” Mama tasa hannu ta karbe bulalar daga gare shi tana fadin, “Ai kuwa dai magana abin a guje ta ne tunda ko kai din ma kana dai fada ne kawai, in ban da kana gudun maganar ai wani iya shegen da ba ayi shi a gabanka kana kallo ba.

Bata kudin mangyadan ni ta sayo min tunda wancan din a gabanka ta kifar dashi, kana kallo.”

“Nawa ne kudin?” Ya tambaya tare da kokarin fiddo da wasu kudin daga aljihun shi, ta ce “Kwalba biyu ne.” daga ni har shi barin abinda muke yi muka yi muka kalli Mama, ni na bar kuka na zuba mata ido shi kuma ya tsaida hannu a aljihunshi ya bar zaro kudin.

“Kwalba biyu ne?” ya bukaci sani, tayi maza ta daure fuska ta ce, “To zanyi mata karya ne ba gata ba? Tambaye ta mana. Ni kam ko da Babana bai yi kuzarin tambayata ba kiris ya rage in bude bakina in karyata Mama, in ce gongoni ne biyu ba kwalba ba.

Sai kuma naga yin hakan ba zai amfane ni da komai ba, tunda ba zai hana Babana biyan kudin kwalba biyun ba, ni kuma sai in sake shiga cikin wani  matsanancin hali, don cewa Mama zata yi na karyatata a gabanshi yana kallo, ko ma ace Inna ta ce ta sani yin hakan tunda ni kullum laifina na Inna ne, ita ke sa ni komai in dai na sharri ne ko kuma danginta.

<< Mijin Ta Ce 2Mijin Ta Ce 4 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×