Yana kuma daidaitan lokacin tashin mu ne ya taso daga gonarshi ya biyo min ta makaranta mu dawo gida tare, da daddare in mun gama abinda muke yi kuma yana duba takarduna yaga aikin da aka yi mana ya yi min gyara kan abin da ban gane ba.
Zaman lafiyan da aka lura aka ga ya samu tsakaninà da mijina ne ya bayyana a cikin gida, wanda ban samu hakan ba sai da na yarda ni ce a kasa shi ne sama da ni, sai da na yarda da barin son raina na koma bin nashi, na koma karbar umarnin. . .