“Ke da masu koya miki iya shege ba zan yi maganin ku, zan sa kafar wando daya daku.” Abinda ya ci gaba da gaya min kenan.
Bayan ya mika wa Mama kudin ita kuwa ta karbe su ta juya tayi tafiyarta, bata sake aiken nawa ba wai kar in je in sake kifar mata, can cikin zuciyata kuwa nasan ba sake saye zata yi ba.
A kullum irin kalaman da Babana kan furta kenan an koya min halin tsiya an yi min hudubar banza, an cusa min dabi’ar da ba za ta amfane ni ba, zai yi maganin mu. . .