Skip to content
Part 41 of 52 in the Series Mijin Ta Ce by Hafsat C. Sodangi

Baba Yahya ya yi matukar murna, ya yi ta addu’a yana sanya albarka, ya rungumi kudi ya tafi dasu, wai zai je yayi duk wani abin da ya dace a gama komai sai bayan tafiyar tashi ne ma maganar ta watsu a cikin gida.

Mama tayi matukar kidimewa, hankalinta ya tashi ta shiga rusa kuka tana zage-zage, Zubaida kuwa sai faman tsalle take yi tana murna tana fadin yau fa ga inda haihuwar ‘ya mace tayi rana.

An mallake ta ita kuma ta mallako wa uwarta mijinta, Gambo kam ba zan iya kwatanta farin cikinta ba, kan ka ce meye wannan yan uwanta har sun cika gida da kuma makwabta, har lokacin Mama ba ta daina kuka da zage-zagen da take yi ba.

Babana yaje ya daga labulenta ya ce mata, ji mana Majadan, kin san dai dama na gaya miki sharadin zamanki a gidan nan yanzu shi ne ki zauna da kowa lafiya, don ba zan iya lamuntar hayaniya ko tashin hankali a cikin iyalina ba.

Don haka in kin ga kina da matsala ko za kije gidan ku ne? Ta yi maza ta suro gyalenta ta yafa ko gama rufe jiki bai yi ba saboda nadewan da yayi tana fadin eh, ai gara min hakan yafi min wannan zaman da nake yi cikin bakin ciki, wulakanci da kuma zalunci.

Ni kam ai ba zan taba yafe aka ba, sai kaga sakamakon…Babana ya bi ta da kallo yace, ke Majadan ki taimake ni in kin je gidan naku kar ki dawo.”

Cak! Mama ta tsaya, ban san tunanin me tayi ba, sai kuma naga ta juyo ta shige dakin nata tayi shiru.

Kwanana biyu a gida na soma zaga dangi yanuwa da kuma abokan arziki, har giyade na tafi da zani kuwa mun tafi ne da su Atika da Aliya da Sa’adatu.

Kan hanyarmu ta dawowa daga Giyade na yi wa yan uwana magana kan halin da Babanmu yake ciki na zaman rashin abin yi, bai kamata mu bar shi a haka ba.

Aliya ta kalle ni cikin natsuwa ta ce, ni kam Anti ban ga abin da ya shigar damu cikin wannan maganar ba, musamman ke matsalarsu shi da matarshi da ‘ya’yansu, mu kam ai ko da yake harkar ma anyi lokacin da abinci ma aka hana shi.

Ba mu koshi da abin da ya faru nayi ta kawo mishi kaji yana ci har ya murmure, ba shi kenan ba?

Gambormu bata cikin matsala, ba kuwa zata sake shiga ba da yardar Ubangii, to su karata mana ko kuwa Anti? Ta zubawa Atika ido, Atika ta tabe baki ta ce, uhn, kyale Anti kawai in kudin sunyi miki yawa ne ki kawo a rinka juya miki su zasu yi amfani a gaba.

Na zuba musu ido ina mamakin yadda ko kadan basa tausayin wahalar da Babanmu ya shiga kan in yi musu wata magana sai Atika ta ce min ni ina ce shi ya kore ki ke da mijinki don taji dadi. Kuje ku kuma ku wulakanta sannan bayan tafiyar taku kin san abin da ya faru? Nayi maza na ce mata a’a, ta ce ina ce sakin Gambo yayi?

Da karfi na kurma wa Atika ihu tare da fadin kar kiyi min haka Atika, ta ce to abar maganar. Ta ci gaba da baiwa Baba nono wanda ni na mika mata shi ta sake waiwayowa tana kallona cikin natsuwa ta ce min.

Ina ce sai da suka yi mishi abin da suka yi mishin ne da ya kori uwarsu a gidan shi ne yazo wai Gambo ta koma, su Baba Yahya suka ki da Alhaji Babba, shi ne mai babban allo ya ce a’a ta koma dakinta ta zauna saboda in muka je gidan mu samu dakin da muka shiga, muka zauna.

Amma ba za ta koma ba sai yaje ya daidaita da matarshi ya dawo da ita tukuna, ya hada su dukansu yayi hakuri ya zauna dasu don sun riga sun zama bangaren rayuwarshi.

Gambo tana da matsala ne? Bata da ita, kullum Yaya Ado yana yi mata aike tana gaya mana ni ta bangare na mijina ba mai sakin kudi ba ne, saboda yana taka tsan-tsan dukiyar ba tashi ba ne ta Baba ce.

Amma ya samar min da wata hanya da ake juya min kudi, ina armfana ina yi mata abin da nake iyawa, Aliya ma tana yi mijin tama yana yi dan ma kuma danta ne tana kuma da ‘yan uwanta ga shagonta na dinki.

Kin ganta da matsala ne? Na girgiza kai a hankali cikin sanyin jiki, can’ cikin zuciyata kuma na gane abinda yasa Ado bai taba furta min abinda ya farun ba, tunda na Gambon ma bai gaya min ba.

Mun dawo gida da yamma gaba daya muka dawo sai dare mazansu zasu zò su dauke su. Sa’adatu tana goye da Umama ni kuma in rungume da Baba akan kafadata, yayin da Atika da Aliya suke rike mana da kayan tsarabar kauye da muka dawo dashi.

A tsakar gida muka samu Babana ya kwance buhun shinkafa yana aunawa can gefe kuma ga doya ya kasata kashi uku, Mama tana tsaye tana Kallon abin da yake yi.

Karo na farko da na ganta a tsakar gida tun da nazo, da sauri naje na kwantar da Baban Atika a daki na dawo na karbi mudun a hannunshi ina aunawa yana nuna min in da zan saka.

Kin ganni ina awo ba Humairah? Na ce mishi eh Baba. Ya ce to daurowa yake yi a daure, Alkali kin gane? Na ce mishi eh, Baba. Ya ce to kin ga wannan buhun shinkafar da wannan doyar kawo min su aka yi kyauta

Na yi wa wanda ya kawo din addu’a, Babana ya amsa da amin. Kafin ya ci gaba da yi min bayani.

Yanzu komai raba shi nake yi a gidan nan in kasa shi kashi uku in baiwa kowa nashi ya adana a wurinshi, saboda Gambo idan na ce zan ajiye ayi amfani da shi gaba daya to sai a biyo dare a kwashe aje a boye ana baiwa kattin banza kin ga haka zai yiwu? Duk da Mama tana wurin bai hana ni cewa a’a ba, a zuciyata na ce ke ki ka koya mishi cewa ana kwashe mishi hatsi ana boyewa.

Shi yasa nake rabona daidai da daidai rabo na adalci in kasa kashí uku kowa ya dauka, ko kuwa? Na ce haka ne, nayi kamar in ce amma da an dan yi wa adalcin kwaskwarima, don ya kara tafiya daidai. Tunda ita Zubaida babu da ko daya a dakinta, ita ita kadaice sai kuma ake yi mata rabo na daidai tsakaninta da Gambota mai ya’ya uku da kuma Mama mai ‘ya’ya uku manyan mutane duk da ita hudu ga kuma jikoki guda bakwai.

Da nayi wani tunanin sai naga to menene nawa a ciki in ja bakina kawai in yi shiru mana, mai ya kare musu a tsakaninsu.

Na daga ido na kalli Mama da tun sanda Babana ya ce mata dauki take kallon kason ta rasa wanda zata zaba. Furfura na gani a girarta da kuma gashin idonta.

Gabana ya fadi na ce ashe a kan yi furfura har gashin ido? Ganin da nayi mata a tsakar gida yau ya kara bayyanar min da sirrin al’amarinta gaba daya.

Gaba daya ta canza, gaba daya tsufa ya yanko ya afka mata, sai ka ce wacce tayi tamanin alhalin kwata-kwata shckarun Mama in tayi da yawa ne zata yi hamsin koda biyu, shekaru biyu kawai da suka wuce ai mama dinta take a cike ga kyau ga zati ga kwalliya, ga iya isa da nuna gadara.

A zuciyata na Kara tabbatarwa kaina da cewar babu abin da yaff bakin ciki nukurkusa dan Adam, musamman ma amce ace tana fuskantar bakin ciki kan haihuwarta da kuma aurenta wanda abin da ya samu Mama kenan a lokaci daya.

Tunda yanzu dai a zahiri yake a bayyane in akwai abin da Babana yake zaune dashi akan lalura to Mama ce de ‘ya’ yanta wadanda a baya kuma su ya so tsawon rayuwar shi yana so yana fifitawa yana yiwa hidina da dawainiyar ba tare da yana tunanin  akwai wasu masu hakki a bayan nasu ba.

Babana yaja tsaki saboda kallon kashin da Mama ke ta yi, ki dauka mana. Yayi maganar cikin tsawa, idonta yana kan na gabanshi, ta nuna da hannunta ga wanda nake so.

Haushinta ya kama shi an ki a baki wannan din na gabanki za ki dauka.

Na ce yi hakuri Baba, bari a kwashe mata wannan din, nasa hannu na soma diban doyar ina kai mata kofar dakinta su Buhari suna karasa mata dashi cikin daki. A zuciyata tunani nake yi a irin iyalin da ke dakain Mama, wannan kason da aka bata kwana nawa zai yi mata? Da na dan yi wani tunani kuma sai naga to Mama ma dai ba abin tausayi ba ce, sai dai kawai mutum ya tausayawa wanda yake tare da ita saboda shi din dan uwanshi ne.

Amma in ba haka ba ai tukunyar gidanmu tana hade ana girki gaba daya na wajo ma in ya shigo gidan mu zai ci ya koshi, Babana yana cikin harkarshi bai da wata matsalar babu.

A wannan lokacin tasa iko ta raka tukunyar ta ce kowa yayi girkin shi don kawai ta ganawa Gambo azaba, ga bakin cikin kishiayr da tasa aka yi mata, ga hakkokinta na aure duk ta danne sai wanda tsananin rabo yasa aka bata,

Amma bai isheta taga bari ta ganawa ‘ya’yanta azabar yunwa.watakia tana ganin ta hakanne kawai zata iya korarta, to wahala kam mun sha daidai gargwado, amma bata yi nisa mai yawa ba sai ta wuce mana ta kuma wucewa uwarmu ta kuma juyo ta dawo mata ta inda bata taba zato ba.

Wai ace mutum bai san yayi adalci ba? An ce a karkace za’a tashi amma shi kullum aikinshi kenan zalunci, cuta, a raina na ce yau kenan ki ka san wannan.

Zai yi magana nayi maza na ce mishi, kayi hakuri Baba. Ya kalle ni cikin natsuwa ya ce, in yi hakuri ta zage ni? Na ce eh ai babu komai, ya ce to shi kenan. Nasa hannu na sake kwashe kashin da yafi dama-dama na kaiwa Zubaida.

Na kirą, Sa’a ta kwashéwa Innarmu na karshen tunda dama kason nashi hawa-hawa ne, wani yafi wani na kuma sân Zubaida yaso ya baiwa babba, ita Mama dan karamin, Gambonmu ta dauki na tsakiya sai Mama taki.

Shi wancan  rabo da kika ga ina yi, na ce eh Baba, ya kale ni yà cc shi ne kaso na gaskiya, da  sauri na ce mishi haka ne Baba.

Ba tare da na tambayi dailin shi na fadin hakan ba, sai naji yace min ita wannan yarinyar ya nuna min dakinta, nayi murmushi na ce Anti? Yayi maza ya ce min eh, na ce eh, ya ce shi yaro yasan babu ne? Nayi maza nå ce mishi a’a Baba bai sani ba, ya ce to kin ga dole a bata da yawa, na ce haka ne. Ya sake nuna min dakin Mama da dan yatsanshi, na ce eh, alamar na gane. Ya rage murya ya ce ni ne zan zauna ina ciyar ta ya’yan gidan wasu da kuma zäurawa?

Nayi maza na ce, a’a Baba, ba zai yiwu ba. Amma itama Habiba auren ya mutu ge? ya girgiza kai nuna alamar bai mutu ba, ya ce amma an samu ta koma da kyar ta haihu a can taje tayi fada da uwar miji akan naman suna.

Daga cikin dakinta Zubaida ta daga murya ta ce fada ko duka? Dukan uwar mijin tayi, nayi kamar ban ji ba, don bana son hirar tamu ta zama sanadin fitina.

To ita Gamborkı ko ban bata ba tana da shi, wani lokaci ma in naga zata kure min Zubaidan ta rasá, shiga wurinta nake yi in debo mata na ce haka né Baba da iyakacin gaskiyata :Sai naga kirkin rabon nashi, don haka ko babu adalci a ciki to da akwai dabara tunda shi adalci ai bai wuce baiwa mai hakki hakkinshi ba.

Rannan muna kwance ni da Gambo akan gadonta bayan su Atika, sun tafi gidajen su sun bar mu, hirą muke yi kan al’amuran da yadda rayuwa ke tafiya, Gambo ta kalle ni tayi murmushi ta ce “Sanda ku ke yara yan kanana a lokacin da nake ganin tanfar abinda ke faruwa a, kaiga ba zai taba wucewa ba.

Kullum ‘naje gaban Mallam mai, babban allo ina kuka zaunar da ni yake yi ya yi ta bani hakuri, sai ya ga natsawata ta dawo jikina.sai ya ce min, wadannan yaran da ki ke haifa Binta ai kawayenki ne.

Kwana nawa ne, in Ubangiji ya amfana miki su za ki ga sun girma sun zama abokan mu’amalar rayuwarki? To amma fa sai kin yi hakuri, sai kin zauna kin yi tarbiyarsu ta yadda Ubangiji zai taimake ki su zama mutanen kirki.

To amma fa sai kin yi hakuri, ki zama ke din bata kanki ki ke yi ba, don kuwa in ki ka yi kuskuren da suka lalace, sai ya girgiza kai nuna alamar abinda zai biyo bayan hakan ba karami ba ne.

To gashi nan a yau, ta sake wani murmushin kafin ta ce na godewa Ubangiji da ya sanya ni na zamo mai bin umarnin iyaye, na ce ban taba sabawa umarnin nasu ba komai zafinshi a kaina.

Ta kalle ni ta ce na kira mijinki dazu don in yi mishi godiya, bai bari mun yi tmaganar ba, na roke ki kiyi mishi biyayya iya iyawarki, ki kuma zauna da kowa nashi bisa gaskiya da adalci.

In hali yasa shi kawo miki abokiyar zama, to duk yadda ki ka kai da kinta kar ki zalunceta, kar ki danne mata hakkinta, na ce mata to Gambo.

Washegari da safe ina tashe da kwanonon dafafiyar kaza mai nonon rakumi da Gambon ta dafa min, wai da ita zan karya. na rike da wayar Gambo ina kokarin kiran Ado, don mu gaisa.

Na kai wayar kunnena ina sauraror ya dauka, na kalli Gambo cikin natsuwa na ce, ni wannän na menene ne Gambo? Ban fa ga alamar za ta yi wani dadi ba.

Gambo ta ce, a to ko babu dadi dai cinyeta aka ce kiyi ki sha romon, na saké kalonta in ji waye Gambo? Ta ce Aliya, ita ta kawo ta ce in dafa miki wai ba za ta iya ba ki da hannunta tana jin kunya.

Ado ya dauki wayar yana jin ni ce ya rage fara’a, na gaishe shi yaya su Bala dai suna lafiya? Ya ce yau ne ya kamata kiyi waya ki tambaye shi? Ai na kuma gane ki wato ke in ki ka samu ‘yan uwanki to zance kuma ya kare, kowa ma za ki iya mantawa da shi.

Na rasa abinda zan yi in wanke kaina, sai na tuna na ce, to kawu ka ki ka sai min waya, zan yi ta bin wayoyin mutane ne ina kiranka, ni kunyar hakan nake ji.

Ya dan ji sanyi, ina Umamah? Ko tana wurin uwarta? Na ce mishi eh, ba ki sani ba Humairah, sai bayan da ki ka taho naje gida kan wani abin da ya kai ni, sai na gane nayi kuskure.

Da sauri na tambaye shi, kuskuren me kayi? Gambo ma ta kallo ni don jin yarda na ambaci kuskuren, ya ce kwanakin da na baki sunyi min yawa, zan koma Dabai wannan satin saboda aikin gonata ki dawo gida kawai.

Gabana yayi matukar faduwa, na ce haba Kawu, yau ne ma fa nake da kwanaki shida a garin ran. Ba za ki dawo din ba kenan? Na ce a’a ba wai ba zan dawo ba ne, amma ni gaskiya bai jira jin gaskiyar tawa ba ya kashe wayar.

<< Mijin Ta Ce 40Mijin Ta Ce 41 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×