Tafiya yayi sosai bai ga alamar kowa ba. Har ya gama dube-dubensa bai sami wata alama da zata nuna masa wata halitta tana rayuwa a cikin wurin ba.
Har zai koma, sai kuma yakai dubansa ga wani kango, dan haka ya tura kai babu ko tsoro.
Ya firgita kwarai ganin Mace a kwance, tana fitar da numfarfashi sama-sama.
"Ruwa...ruwa.."
Zayyad ya dubi gefensa akwai ruwa a wani bokiti. Ya dibo da sauri ya daga kanta babu ko kyama ya ba ta. Bayan tasha ne ta saki ajiyar zuciya.
"Me ke damunki?"
Ya tambayeta cike da mamaki da. . .