Skip to content
Part 1 of 4 in the Series Muryar Dalili by Haiman Raees

Aure

 Duniyar Labaran Haiman 06

 Godiya

 Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah maɗaukakin sarki. Tsira da amincinSa su ƙara tabbata ga Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam. Da alayensa da sahabbansa, da jama’ar gidansa, da sauran mutanen kirki daga cikin al’ummarsa baki ɗaya.

 

Sadaukarwa

 Na sadaukar da wannan littafi ga gwanaye kuma fasihan mawaƙan ƙasar Hausa, su ne Aminu Alan Waƙa, Mu’azu Haɗeja, Sa’adu Zungur, Farfesan Waƙa, Nura M. Inuwa, Sani Sabulu, Fati Nijar da kuma Abubakar Sani.

 

Jinjina Ta Musamman

 Ina miƙa jinjina ta musamman ga dukkan malamaina daga kowane fanni na karatu da kuma rayuwa. Allah ya saka da mafificin alheri duniya da lahira. Amin.

 

Ana Tare

 Ina miƙa saƙon gaisuwa ga ɗaukacin membobin ƙungiyar Lafazi Writers Association. Musamman shugabanta Sadik Abubakar, Surayya Ɗahiru, Mukhtar Hussaini, Fauziyya Sani Jibrin, Aseeya Muhammad, Ummu Khamilat, Usaina Salis da duk sauran membobin wannan ƙungiya tamu mai albarka.

 

Gargadi

 Ba a yarda wani, wata ko waɗansu gungun mutane su yi amfani da wani ɓangare ko sashe na wannan littafi ba sai da izinin marubucin a rubuce.

 MATASHIYA 

 A wata duniyar can ta daban, akwai ƙasashe, mutane, dabbobi, addinai da al’adu masu kama da irin namu, suna kuma da zubi irin namu. Ko da yake al’amuran da ke faruwa a cikin wannan duniya sun yi kamanceceniya da irin waɗanda ke faruwa a tamu duniyar, wasu al’amuran sun sha bamban da namu. Akwai labarai masu tarin yawa da suka faru a cikin wannan duniya masu tarin abubuwan al’ajabi da ban mamaki, wataƙila ma mai karatu ya yi tunanin a tashi duniyar suke faruwa, amma a zahiri al’amuran na faruwa ne a wata duniyar can ta daban. A cikin wannan duniyar mai kama da tamu, an yi wani mawaƙi mai hikima da ke cewa… 

01.

Da sunan Allahna da ya yo ɓaure

Al-Ƙadiru da ya yi mu ta silar aure

Ya halasta mana ni’imar yin aure

Ya ba mu umurni da mu yo aure

Ya sa zaman rayuwa ya gyaru ta silar aure.

02.

Tsira da aminci su ƙaru ga Manzona

Gwarzona da ya zamo sirrin shiriyarmu

Al-Mustapha gatan iyaye da kakannina

Sannu amintaccen Makka da Madina

Kai ne ka ja hankalinmu akan aure.

03.

Gidan da babu aure ya zama ƙyaure

Da zaman da babu aure gara ɓaure

Zaman samari ba aure sai an jure

Kowace ‘ya mace burinta yana aure

Albarkar Allah ta yawaita cikin aure.

04.

Nutsuwar matasa shi ne su yi aure

Neman ilimi mun san bai hana aure

Neman kuɗi ribarsa a yo aure

Soyayyar gaskiya ribarta tana aure

Masoyan gaskiya burinsu su yo aure.

05.

Kowane Uba yana son ɗansa ya yi aure

Kowace Uwa tana so ɗiyarta ta yi aure

Kowane matashi burinsa ya yo aure

Kowace matashiya muradinta ta yo aure

Jama’ar gari suna son ganin ana ta aure.

07.

Wannan ke tabbatar da kimar aure

Allahu sarkinmu ya darajta mai aure

Manzonmu Aminu ya faɗi girman mai aure

Mutanen duk garinmu suna martaba aure

Addinan duniya kaf na daraja aure.

08.

Babu wata ƙasa da ba ta girmama aure

Babu wani gari ko birni da ba a martaba aure

Babu wata ƙabila da ke ƙyamar aure

Babu wani addini da ya yi hani da aure

Wannan shi ne tabbacin ni’imar aure.

09.

Ko da kana da aure kana iya ƙara aure

Masu mata ɗaya na son ƙara aure

Masu mata biyu an yarda su ƙara aure masu mata uku na da damar ƙara aure

Amma masu mata huɗu sun cike ƙofar aure.

10.

Tun da kowa ka bincika yana son aure

Sai ka ɗauka kowa na iya riƙon aure

Sai ka ɗauka kowa buri nai a riƙe aure

Ka yi tsammanin babu mai shikin aure

To amma yau kisan wulaƙanci ake yi wa aure.

11.

Wani aure a shekara ɗaya an rabu

Wani aure a wata ɗaya ka ji babu

Wani auren cikin sati guda an rabu

Wani ma cikin dare ɗaya an rabu

Shin mi ad dalilin haka ne Malam Habu?

12.

Rashin ƙauna ce ko tilas ne?

Rashin kuɗi ko na abinci ne?

Rashin amana ne ko gaskiya?

Sakarci ne ko kuma rashin lafiya?

Na rasa gane mazan ko matan ne?

13.

A kullum fa jama’a auren ake yi

Kuma kullum mutuwa yake yi

Ga zawarawa birjik bisa layi

Wasu sun kira shi da sauyin yanayi

Wasu kuma sun maishe shi ya yi.

14.

Wasu ƙabilun dai ba sa haka nan

Yawanci cikinmu ake yin haka nan

Mun sa ran saki ya halasta a yi

Amma sai in da dalili ake yi

Dalili mai ƙarfi ke sa a yi.

15.

Mutuwar aure tai yawa mu duba

Niyyarmu da aiyuka mu gyara

Mu sani ibada ce mu duka

Muke yi wa Allah mai duka

Adalci da biyayya mu ɗauka.

16.

Allahu ka kawo mana sauƙi

Matanmu su zauna a ɗaki

Su daina yawon bariki

Da shigar nan ta rashin kirki

Su yi zaman su a gidan aure.

Muryar Dalili 2 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×