Skip to content
Part 17 of 30 in the Series Tambaya by Haiman Raees

Mutuwa

01

Sarki Allah, ubangijina mai mutuwa 

Ya Mannanu, da sunanKa ni zan fara 

Sarkin mutuwa, da duk komai na rayuwa 

Allahu gwani, yai duniya kuma yai lahira 

Al-ƙaliƙu Ya As-Samadu, Kai ke da rayuwa 

Kai ka yi ranmu, kuma kai ne ka yo mutuwa. 

02.

Salati ga manzo, Muhammadu Rasulullah 

Ɗan lele, a wurin Allah kai ne Nurullah 

Kai ne na gaba, a cikin halittun Allah 

Ya Manzon mu, ka cece mu a gaban Allah 

Ka zamo jin ƙai, a lahira bayan mutuwa. 

03.

Allahu gwani, bisa hikima da buwayarSa 

Ya yi rayuwa, Ya yi mutuwa bisa ikonSa 

Ya sa rayuwa, ta zamo gwaji ga bayinSa 

Ya sa mutuwa, ta zam izina ga bayinSa

Domin bayinSa, su sam darasi kan rayuwa. 

04.

Amon mutuwa, yana yawo tamkar sauti 

Sautin mutuwa, yana yawo har kan titi 

Titin rayuwa, mutuwa tuni tai fenti 

Fentin mutuwa, ya yi ado a duk rayuwa 

Rayuwar kowa, ko ba ka so ka san mutuwa. 

05.

Mai yin tafiya, ka bincika ya san mutuwa 

Mai saurare, in da hankali yasan mutuwa

Mai karatu, da nazari ka san mutuwa 

Mai daraja, da musaki kowa yasan

Mutuwa 

Hakanan kowa, in ka tambaya yasan mutuwa. 

06.

Ka yi taimako, ka ƙi taimako akwai mutuwa

In ka gyara, ko ka ɓata da akwai mutuwa 

Kai zalunci, ko adalci da akwai mutuwa 

Ka yi gaskiya, ko ha’inci da akwai mutuwa 

Ko mai muka yi, mu dai sani da akwai mutuwa. 

07.

Ina tajiri, mai dukiya da samun duniya 

Ina shugaba, da anka ba mulkin duniya 

Ina malami, da anka ba sanin duniya 

Ina manomi, da anka ba ribar noma a duniya 

Ko a kasuwa, ko ina kake dai a duniya. 

08.

Ina matashi, mai samartaka kana tashe 

Ina budurwa, mai budurtaka kina tashe 

Ina ɗan yaro, da yanzu yake ƙuruciyarsa 

Ina jariri, da yanzu yake fara yin rayuwar sa 

Har ma na ciki, mutuwa tana iya samun sa. 

09.

Ina talaka, da bai da komai sai ransa 

Ina faƙiri, da bai da komai sai tufarsa 

Ina mai kyawu, da ke jiji da kyawunta 

Ina mai diri, da ke taƙama da dirinta 

Ranar mutuwa, wannan ba za a duba ba. 

10.

Ko ka shirya, ɗan uwa ko ba ka shirya ba 

Ko kin shirya, ‘yar uwa ko baki shirya ba 

Ko na shirya, ‘yan uwa ko ban shirya ba 

Ko kun shirya, ‘yan uwa ko ba ku shirya ba 

Ko mun shirya, ‘yan uwa ko ba mu shirya ba. 

11.

Da lokaci yayi, tafiya fa ba mai hanawa 

Ko da Ummi, ko Baba ko ko ‘yan uwa 

Wane mata, ko ‘ya’ya, basu hanawa 

Ba batun maƙiya, masoya ma basu hanawa 

Haka za ka tafi, ana kallo ka yi macewa. 

12.

Aikin da ka yi, komai kyawu ko muninsa

Shi za ka taras, a yadda ka yi shi da siffarsa 

Hali na ƙwarai, ibada da imani ko akasin sa 

Kai adalci, zalunci ko makamantansu 

Su za ka taras, makwancinka kai ka shirya shi. 

13.

Allah ka shirye mu, ka sa kuskure mu gyaggyara

Ka yo afuwa, laifukanmu ka sa a wawwanke

Ka yo yafiya, zunubanmu duka a kankare

Ka yi mana tsari, azaba ta kabari ka tuttunkuɗe

Ka yo rahama, tabbas ita rahamar ai taka ce.

14.

Ranar mutuwa, idan ta zo ka sa mu dace 

Kalmar daraja, furtata ka sa mu dace 

Da imani, cikin zuciya kar ya kuɓuce 

Har Aljannah, mu sam tafiya a cikin dace 

Ka haɗa mu, da Manzon mu abin kwatance. 

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 2

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Tambaya 16Tambaya 18 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×