Deena ta manta da zuciya na da idanun da ganinsu yake da tasiri fiye da na idanu, domin ita tana tsara abu ne a yadda take so kafin ta karɓe shi, don haka rashin idanu ba zai hana Deeni son Rahila ba madamar zuciyarsa ta amince da ita, domin nagartar Rahila ba wai a idanu kaɗai ta tsaya ba, nagarta ce mai sanya nutsuwa a zuciyar duk wanda mu'amala ta haɗa shi da ita, wanda kuma Deenin da take gode ma Allah da baya gani ya san haka, kawai dai ra'ayinsa a kan soyayya da. . .